Ahmad Fagam">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home DAGA BIRNIN SIN

COVID-19: Rayuwar Amurkawa Na Cikin Tasku

by Ahmad Fagam
January 4, 2021
in DAGA BIRNIN SIN
2 min read
COVID-19: Rayuwar Amurkawa Na Cikin Tasku

WASHINGTON, DC - SEPTEMBER 22: Chris Duncan, whose 75 year old mother Constance died from COVID on her birthday, photographs a COVID Memorial Project installation of 20,000 American flags on the National Mall as the United States crosses the 200,000 lives lost in the COVID-19 pandemic September 22, 2020 in Washington, DC. The flags are displayed on the grounds of the Washington Monument facing the White House. (Photo by Win McNamee/Getty Images)

WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Masu hikimar magana suna cewa “tsalle guda ake a fada rijiya sai an yi dubu ba a iya fita ba”. Tun bayan bullar annobar cutar numfashi ta COVID-19 a farkon shekarar da ta gabata an yi ta samun bayanai masu cin karo da juna a tsakanin mahukuntan Amurka, lamarin da ya janyo rudani da cece-ku-ce a tsakanin al’ummar kasar wacce ke ikirarin tutiya da tsarin mulki irin na demokaradiyya. Koda yake, tsarin mulkin demokradiyya ya sahhalewa al’umma ’yancin aiwatar da rayuwarsu yadda suke so. To amma game da yadda shugabannin Amurka suka yi sakaci da rikon sakainar kashi kan batun annobar tun a farkon lamari shi ne musabbabin da ya jefa rayuwar al’ummar kasar cikin mummunan tasirin annobar ta COVID a halin yanzu. Bisa alkaluma na baya bayan nan da cibiyar nazarin kimiyya ta CSSE dake jami’ar Johns Hopkins ta Amurka ta fitar, ya zuwa yammacin ranar Asabar din da ta gabata, adadin Amurkawan da annobar COVID-19 ta hallaka ya zarce 350,000. Yayin da yawan mutanen da suka kamu da cutar a kasar ya kai miliyan 20 da dubu 400. A cewar alkaluman, jahar New York ta yi hasarar rayukan mutane 38,273, ita ce ke sahun gaba na yawan mutanen da cutar ta kashe a Amurka. Texas tana matsayi na biyu na yawan mutanen da suka mutu 28,338, sai jahar California dake bi mata baya da yawan mutuwa 26,542, Florida ta rasa mutane 21,890, kamar yadda alkaluman CSSE suka nuna. Jahohin da yawan mutuwarsu ya zarce 10,000 sun hada da New Jersey, Illinois, Pennsylvania, Michigan, Massachusetts da jihar Georgia. Amurka ce kasar ta annobar COVID-19 ta fi yiwa barna a duk duniya, ita ce take da adadi mafi yawa na mutanen da suka mutu a sanadiyyar cutar da kuma mutanen dake kamuwa da cutar, inda take da kashi 24 bisa 100 na yawan masu kamuwa da cutar a duk duniya, kana tana da kashi 19 na yawan mutanen da cutar ta kashe a duniya baki daya.

Adadin Amurkawan da COVID-19 ta kashe a cikin kwanaki 19 ya zarce 50,000, bayan cutar ta kashe mutane 300,000 ya zuwa ranar 14 ga watan Disambar shekarar 2020. Sai dai wani abu mai ban tausayi da juyayi shi ne yadda masana suka yi hasashen mummunar hasarar rayukan da za a samu na Amurkawa nan da wasu ’yan kwanaki ko watanni masu zuwa, kamar yadda cibiyar kiwon lafiya da bincike ta jami’ar Washington ta yi hasashen cewa, yawan mutunen da COVID-19 za ta kashe a kasar Amurka zai iya kaiwa 567,195 ya zuwa ranar 1 ga watan Afrilun 2021. Hakika, ya kamata shugabannin Amurka su kara himma domin kada wankin hula ya kai su dare game da wannan masifaffiyar cuta. (Ahmad Fagam)

samndaads
SendShareTweetShare
Previous Post

An Kawar Da Talauci Ta Hanyar Kiwon Tumaki A Gundumar Huan Dake Lardin Gansu Na Kasar Sin

Next Post

Masar Ta Baiwa Kamfanin Sinopharm Lasisin Amfani Da Allurar Rigakafin COVID-19 Domin Bukatun Gaggawa

RelatedPosts

Hadin Gwiwar Sin Da Afrika Kan Yaki Da COVID-19 Na Kara Fadada

Hadin Gwiwar Sin Da Afrika Kan Yaki Da COVID-19 Na Kara Fadada

by Ahmad Fagam
14 mins ago
0

Wani masanin harkokin tattalin arziki na kasar Habasha, Costantinos Bt....

Sanya Takunkumi Kan Pompeo Da Sauran Wasu Amurkawa 27 Abu Ne Da Ya Dace

Sanya Takunkumi Kan Pompeo Da Sauran Wasu Amurkawa 27 Abu Ne Da Ya Dace

by Ahmad Fagam
16 hours ago
0

Kwanan nan, gwamnatin kasar Sin ta sanar da sanya takunkumi...

Jarin Da Sin Ta Zuba Kai Tsaye A Ketare A Shekarar 2020 Ya Karu Da 3.3%

Jarin Da Sin Ta Zuba Kai Tsaye A Ketare A Shekarar 2020 Ya Karu Da 3.3%

by Ahmad Fagam
16 hours ago
0

Kididdigar da ma’aikatar kasuwanci ta kasar Sin da hukumar kula...

Next Post
Masar Ta Baiwa Kamfanin Sinopharm Lasisin Amfani Da Allurar Rigakafin COVID-19 Domin Bukatun Gaggawa

Masar Ta Baiwa Kamfanin Sinopharm Lasisin Amfani Da Allurar Rigakafin COVID-19 Domin Bukatun Gaggawa

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version