Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Covid-19: Sakamakon Gwaji Ya Wanke Ganduje Da Uwargidansa

by
2 years ago
in RAHOTANNI
2 min read
Covid-19: Sakamakon Gwaji Ya Wanke Ganduje Da Uwargidansa
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Gwamnan Jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje da Mai Dakainsa, Farfesa Hafsat Abdullahi Ganduje, sakamakon gwajinsu ya nuna ba sa dauke da cutar Cobid-19 dake addabar duninya, kamar yadda Babban Daraktan Yada Labaran Gwamnan Jihar Kano, Abba Anwar ya shaida wa Jaridar LEADERSHIP A YAU.

“Muna yi wa Allah godiya, bisa wannan sakamako wanda ya nuna ba ma dauke da wannan cuta. Haka Allah ya so, kuma su ma wadanda ke dauke da ita za mu cigaba da yi musu addu’ar samun saukin warwarewa daga cutar ba tare da la’akari da bangaranci, kabila, addini ko kuma siyasa ba,”in ji shi.

Sannan, Gwamnan ya yi addu’ar fatan cigaba da samun kariya daga wannan cuta ta Cobid-19 a Jihar Kano, kasa da ma duniya baki-daya. “Haka kuma, kamar yadda muke kara cigaba da neman tallafi, dole ne mu tabbatar da cigaba da sauraren shawarwarin kwararru ta fuskar harkokin lfiya tare da yin aiki tare.”

Labarai Masu Nasaba

Ranar Iyali Ta Duniya: Ma’aikatar Jinkai Za Ta Kai Wa Iyalai 30 Daukin Kuncin Rayuwa

Rikicin Ukraine Ya Haifar Da Karin Tsadar Kayan Abinci A Nijeriya —Rahoton NBS

Gwamna Ganduje, ya bukaci al’umma da su cigaba da wanke hannu, amfani da na’urar tantancewa, tabbatar da tsaftar muhalli, kaucewa dukkanin wani cunkoson mutane, musamman a kasuwanni da sauran wuraren haduwar al’umma da sauransu.

Ya kara da cewa, “zama a cikin gidaje ne mafi cancanta tare da kare kai. Haka kuma, ya bukaci al’ummar Nijeriya da su yi kokarin kulawa da umarnin da Gwamnatin Tarayya ta bayar da sauran matakan da ya kamata a kiyaye, domin dakile yaduwar wannan cuta.”

Bayan karbar sakamakon gwajin, Gwamna Ganduje ya tabbatar da cewa Gwamnatinsa za ta cigaba da daukar matakan dakile yaduwar cutar Cobid-19, wanda aka fara da shawarwarin masana, kwararru da sauran masu ruwa da tsaki, wadanda suka bayar da muhimman shawarawari, domin samun kariya daga wannan cuta da kuma dakile yaduwarta.

“Ya zama wajibi mu tabbatar da yakar wannan cuta ta kowanne bangare, domin samun ingantacciyar al’umma. Muna kara yi wa Allah godiya da har zuwa wannan lokaci babu wani rahoton bullar wannan cuta a Jihar Kano. Muna rokon Allah Ya kare sauran jihohin da ke kasar nan da sauran kasashen duniya.”

Ganduje ya jaddada aniyarsa ta cigaba da tabbatar da ganin ana yin aiki da umarnin da Gwamnati ta bayar na rufe iyakoki tare da tabbatar da cewa, dukkanin masu karya wannan doka an kama su, an kuma gurfanar da su gaban shari’a tare da girbar abinda suka shuka.

Sannan ya kuma yi amfani da wannan dama, inda ya gode wa Kwamitin kar-ta-
kwana kan wannan cuta ta Cobid-19, wanda Mataimakin Gwamnan Jihar Kano, Dakta Nasiru Yusif Gawuna ke Shugabanta, wanda Farfesa Abdulrazak Garba
Habibu ke taimakawa da sauran Mambobin Kwamitin, bisa kokarin da suke na magance matsalar cutar tare da sauran Jami’an lafiya, a cewar Gwamnan.

“Muna kara mika sakon godiyarmu ga Kwamitin asusun tallafi, karkashin Shugabancin Farfesa Muhammad Yahuza Bello, Mataimakin Shugaban Jami’ar
Bayero da ke Kano da mai taimaka masa Alhaji Tajuddeen Dantata da kuma sauran wadanda suka aika da gudunmawarsu irin su Alhaji Aminu Dantata, Alhaji Aliko Dangote, Alhaji Abdussamad Isyaka Rabu, Mista Lee, Bankin UBA da sauran daidaikun mutane da kungoyoyi”, in ji Ganduje.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Har Yanzu Ma’aikatan Kananan Hukumomin Neja Ba Su San Matsayin Albashin Watan Maris Ba

Next Post

COVID-19: Tallafin Buhari Ga Talakawa, ‘Yar Manuniya Ce Ga Tausayinsa -PSC

Labarai Masu Nasaba

Ranar Iyali Ta Duniya: Ma’aikatar Jinkai Za Ta Kai Wa Iyalai 30 Daukin Kuncin Rayuwa

Ranar Iyali Ta Duniya: Ma’aikatar Jinkai Za Ta Kai Wa Iyalai 30 Daukin Kuncin Rayuwa

by
52 mins ago
0

...

Rikicin Ukraine Ya Haifar Da Karin Tsadar Kayan Abinci A Nijeriya —Rahoton NBS

Rikicin Ukraine Ya Haifar Da Karin Tsadar Kayan Abinci A Nijeriya —Rahoton NBS

by
21 hours ago
0

...

Cafke Wadanda Ake Zargi Da Kisan Deborah: Zanga-zanga Ta Barke A Sokoto

Cafke Wadanda Ake Zargi Da Kisan Deborah: Zanga-zanga Ta Barke A Sokoto

by Abba Ibrahim Wada
3 days ago
0

...

Cafke Wadanda Ake Zargi Da Kisan Deborah: Zanga-zanga Ta Barke A Sokoto

Cafke Wadanda Ake Zargi Da Kisan Deborah: Zanga-zanga Ta Barke A Sokoto

by Abba Ibrahim Wada
3 days ago
0

...

Next Post
COVID-19: Tallafin Buhari Ga Talakawa, ‘Yar Manuniya Ce Ga Tausayinsa -PSC

COVID-19: Tallafin Buhari Ga Talakawa, ‘Yar Manuniya Ce Ga Tausayinsa -PSC

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: