Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home RAHOTANNI

Cutar Kyanda Ta Bulla A Taraba

by Tayo Adelaja
September 18, 2017
in RAHOTANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Mohammad Shafi’u,  Yola

Asusun kula da yara na Majalisar Dinkin Duniya wato UNICEF ya shirya taron fadakar da jama’a a jihar Taraba sanadiyar bullar cutar kyanda.

An tabbatar da bullar cutar kyanda a kananan hukumomi goma sha hudu daga cikin goma sha shida da ke jihar Taraba da ya yi sanadiyyar mace-macen yara da dama ‘yan kasa da shekaru goma.

Babban jami’in asusun kula da yara na Majalisar Dinkin Duniya, MDD, a jihar Taraba, Dakta Zarto Philip ya sanar da haka a wani taron gaggawa da shugabannin kananan hukumomi, sarakunan gargajiya da jami’an kiwon lafiya mataki na farko gabannin soma aikin rigakafin cutar kyanda a jihar.

Dakta Zarto Philip ya ce a jihohin arewa maso gabas yara 100 daga cikin dubu 25 ke mutuwa sakamakon kamuwa da cutar kyanda wanda ya danganta da dalilai na rashin tsaro sakamakon matsalar Boko Haram da kuma tirjiya da ake alakantawa da addini da al’adun gargajiya.

Uwar gidan gwannan Jihar Taraba Barrista Ana Darius Dickson Ishaku ta ce akwai bukatar sadaukar da kai a bangaren jami’an kiwon lafiya mataki na farko da ke aiki a yankunan karkara ba tare da la’akari da matsalar yanayi ko kudaden alawus da ake biyansu ba wajen aiwatar da aikinsu don kada su cutar da wadanda ke zaune a kan tsaunuka ko koramu inda babu hanyar mota.

Da yake bayanin kaifin matsalar bullar cutar kyanda a yankunan karkara, sakataren kungiyar shugabannin kananan hukumomi ta kasa reshen jihar Taraba Honorabul Idi Mali ya fadawa cewa ana samun karuwar mutuwar yara a cibiyoyin kiwon lafiya mataki na farko a ‘yan kwanakin nan sakamakon bullar cutar.

Kan gudummawar da ya dace sarakunan gargajiya su bayar wajen yaki da cutar, Galadiman Muri Alhaji Lamido Abba ya ce zasu yi Yekuwa sako-sako da lugu-lungu har sai sun tabbatar talakawansu sun rungumi shirin allurar rigakafin cutar.

Alkalumma da asusun kula da yara na Majalisar Dinkin Duniya, MDD, sun nuna an samu karuwar kamuwa da mace-macen Yara ‘yan kasa da shekara goma daga miliyan dari da casa’in a 2014 zuwa miliyan dari biyar da ashirin da bakwai a 2016 wanda a bana ake kiyasar na iya dara hakan.

SendShareTweetShare
Previous Post

An Damfari Wata Bakatsiniya A Saudiyya

Next Post

An Kafa Kwamitin Da Zai Sa Ido Kan Hakar Ma’adanai

RelatedPosts

‘Goyon Bayan Da Al’ummar Fagge Suka Bamu Da Shawarar Jagororinmu Ya Sa Muka Sami Nasara’

‘Goyon Bayan Da Al’ummar Fagge Suka Bamu Da Shawarar Jagororinmu Ya Sa Muka Sami Nasara’

by Sulaiman Ibrahim
2 days ago
0

Daga Ibrahim Muhammad Kano. Sakataren mulki na karamar hukumar Fagge...

Na Sadaukar Da Albashina Ga Marayu – Ekene   

Na Sadaukar Da Albashina Ga Marayu – Ekene  

by Muhammad
3 days ago
0

Daga Abubakar Abba, dan takarar Kujerar shugaban karamar hukumar Chikun...

NAF

Martani: Babu Ragowar Jirginmu Da Ya Bace A Bama – NAF

by Muhammad
4 days ago
0

Daga Mahdi M. Muhammad, An ja hankalin rundunar sojin saman...

Next Post

An Kafa Kwamitin Da Zai Sa Ido Kan Hakar Ma’adanai

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version