Da A Ce Ni Ba Dan Fim Ba Ne, Da Na Zama Malamin Addinin Musulunci -Baba Rabe
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da A Ce Ni Ba Dan Fim Ba Ne, Da Na Zama Malamin Addinin Musulunci -Baba Rabe

byRabilu Sanusi Bena
7 months ago
Fim

Jarumin Kannywood Abubakar Waziri ko kuma Baba Rabe kamar yadda wasu ke kiranshi ya bayyana batutuwa da dama da su ka shafi jaruman fim, yadda suke gudanar da rayuwarsu ta yau da kullum da kuma yadda mutane ke kallonsu, Baba Rabe a wata hira da ya yi da DW ya ce akwai bukatar malamai su shigo cikin harkar Kannywood ka’in da na’in domin yanzu wani lokaci ne da mutane sunfi mayar da hankalinsu wajen kallon fina-finai fiye da wa’azozin malaman musulunci.

Abubakar Waziri wanda ya ce shi haifaffen birnin Zaria ne a Jihar Kaduna, ya yi karatu a makarantu da dama har ma da Jami’ar Ahmadu Bello inda ya samu shaidar kammala karatun Diploma a bangaren Al’adun gargajiya, bayan harkar fim ni ma’aikacin gwamnati ne inda nike aiki da ‘Abuja Council For Art And Culture’, amma tunda farko na fara aiki a Jami’ar Ahmadu Bello a matsayin dan wasan kwaikwayo a sashen Al’adun Gargajiya na makarantar inji shi.

  • Nijeriya Za Ta Nuna Gyare-gyaren Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu A Taron Kasuwanci A Faransa
  • Taro Na Uku Na Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Sin Ya Yi Zama Na Biyu

Ya kara da cewar kafin shiga masana’antar Kannywood na yi tafiye tafiye da dama wajen wakiltar Nijeriya a kasashe daban-daban da su ka hada da Amurka, China, Afrika Ta Kudu, Korea Ta Arewa, Korea Ta Kudu da sauran kasashen waje duk dai a fannin raye raye da wasan kwaikwayo, kuma cikin ikon Allah yanzu kuma gani a masana’antar Kannywood a matsayin jarumi.

Da yake amsa tambaya a kan yadda wasu ke daukar jaruman masana’antar Kannywood a matsayin wasu mutane masu girman kai, Abubakar Waziri ya ce ko kusa wannan magana ba gaskiya bace, misali mu jaruman fim da muka kasance abinda bature ke kira ‘public figure’, muma muna da abubuwan da muke son aiwatarwa a rayuwar yau da kullum, idan na fito daga gida idan ba na yi fuska na yi tafiya ta ba, mutane da dama kan zo wajena domin daukar hotuna ko kuma yi mani tambayoyi a kan wasu fina-finai da na yi.

Idan hakan ta faru wani lokacin mutum ba zai samu damar da zai aiwatar da abin da ya fito gida domin ya aiwatar ba, don haka kamata yayi mutane su fahimce mu a maimakon su koma gefe su na kiranmu da masu ji da kai, Waziri ya ci gaba da cewar wannan dalili ne ya sa mutane ke yi masu kudin goro a duk lokacin da wani daga cikinsu ya aikata abinda ba daidai ba a maimakon a dora ma wanda ya yi laifin shi kadai sai ace ai duka yan fim haka suke.

Daga karshe Abubakar Waziri Bado ya yi kira da a maimakon malamai su koma gefe su na zagi yan fim kamata ya yi ace su shigo cikin harkar a dama dasu, domin kuwa yanzu wani lokaci ne da ake ciki inda da dama mutane sun fi kallon fina-finai fiye da yadda su ke kallon karatuttukan malaman addini, saboda haka su shigo a hada karfi da karfe wajen kara tsaftace wannan masana’antar don kuwa ni ma kaina da ace ba jarumin fim bane ni , to da tabbas zan zama malamin addinin musulunci saboda ina matukar sha’awar ganin al’umma ta gyaru.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano
Nishadi

Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano

October 6, 2025
An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana
Nishadi

An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

October 4, 2025
Daga Kallon Fina-finan Indiya Na Samu Sha’awar Fadawa Kannywood – Kamalu Mijinyawa
Nishadi

Daga Kallon Fina-finan Indiya Na Samu Sha’awar Fadawa Kannywood – Kamalu Mijinyawa

September 28, 2025
Next Post
Yaushe Liverpool Za Ta Lashe Gasar Firimiyar Ingila?

Yaushe Liverpool Za Ta Lashe Gasar Firimiyar Ingila?

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version