Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Bayar Da Belin Dakta Idris Abdul'aziz Bisa Sharadi Uku
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Bayar Da Belin Dakta Idris Abdul’aziz Bisa Sharadi Uku

byKhalid Idris Doya
2 years ago
Dakta Idris

Kotun Majistire mai lamba ta daya da ke Bauchi ta amince da bukatar bayar da belin Dakta Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi bisa sharadin guda uku.

 

Idan za a tuna dai, ‘yansandan sun gurfanar da Malamin ne a gaban kotun bisa zarginsa da tada zaune tsaye da ka iya barazana ga zaman lafiyan jama’a. Kuma hakan ya biyo bayan korafin da kungiyar Fitiyanul Islam ta shigar ne a kansa.

  • Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Tasa Ƙeyar Dr. Idris Kan Zargin Kalaman Batanci Ga Manzon Allah

Da ya ke yanke hukunci kan bukatar belin, Mai Shari’a Abdulfata Baba Shakoni, ya ce, ya amince da bukatar belin malamin bisa sharadi guda uku, na farko zai kawo Hakimi, na biyu Babban Sakatare da ke aiki a karkashin Gwamnatin jihar Bauchi da kuma wani Malami da ke kwayan Bauchi.

 

Kazalika, ofishin Antoni Janar kuma kwamishinan shari’a ta jihar Bauchi sun bukaci kotun da ta amince musu su amshi ragamar karar daga hannun ‘yansanda domin cigaba da Shari’ar.

 

Daga bisani kotun ta amince da wannan bukatar.

 

Da ya ke karin haske kan hukuncin, daya daga cikin lauyoyin da suke kare malamin, Barista Sadik Abubakar Ilelah, ya nuna farin cikinsu bisa samun belin malamin tare da cewa insha Allahu za su cika sharudan da Alkalin ya gindaya.

 

Da yake bayani kan amsar ragamar karar da suka yi, daya daga cikin lauyoyin a ma’aikatar shari’a ta jihar Bauchi, Aliyu Ibn Idris, ya ce, “Shi Antoni Janar na jiya ko na tarayya yana da dama da dalili ba dalili ya shiga cikin kara.”

 

“Antoni Janar ya shigo ya karbi Kes ba sabon abu ba ne. Iyakaci abun da za a duba shigowar tamu za ta haifar da adalci ko ba za ta haifar da adalci ba. Insha Allahu za mu yi iyaka abun da za mu yi a wanzan da adalci a kai,” Inji shi.

 

Sannan, ma’aikatan shari’an ta bukaci ‘yanda da su ba su kundin Shari’ar da sauran abubuwan da suka hada wajen shigar da cajin domin nazarin akwai bukatar canzawa ko a’a.

 

Daga bisani dai Alkalin ya dage shari’ar zuwa ranar 24 ga watan nan da muke ciki domin cigaba da shari’a.

 

Wakilinmu ya labarto cewa an sake komawa da malamin zuwa gidan yari har zuwa lokacin da za su cika sharadin belin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu
Labarai

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Next Post
Taimkon Juna Tushen Dangantakar Sin Da Afrika

Taimkon Juna Tushen Dangantakar Sin Da Afrika

LABARAI MASU NASABA

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version