Da Dumi-dumi: 'Yansanda Sun Tabbatar Da Yin Garkuwa Da 'Yan Hidimar Kasa A Jihar Ribas
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Dumi-dumi: ‘Yansanda Sun Tabbatar Da Yin Garkuwa Da ‘Yan Hidimar Kasa A Jihar Ribas

bySulaiman
2 years ago
Garkuwa

Rundunar ‘yansandan jihar Ribas ta tabbatar da sace wasu ‘yan hidimar kasa (NYSC) wadanda har yanzu ba a tantance adadinsu ba akan titin Gabashi zuwa Yammaci (East-West) da ke jihar Ribas.

Sace Matasan NYSC din na zuwa ne kasa da sa’o’i 24 bayan da shugaban karamar hukumar Emohua ta jihar, Dakta Chidi Lloyd, ya ayyana neman wani matashi mai suna Onuigwe Wodi mai shekaru 22 ruwa a jallo har da ladan Naira miliyan 1 kan duk wanda ya bayyana in da yake, bisa samunsa da hannu wajen kashe ‘yansanda, mu’amala da kungiyar asiri, garkuwa da mutane da fashi da makami a hanyar Gabashi zuwa Yammaci da ke jihar.

  • Na Yi Nadamar Taimakawa Tambuwal Zama Kakakin Majalisa – Gbajabiamila

Lloyd ya kuma sanar da dakatar da biyan albashin jami’an ‘yan banga ta EMOVIS sakamakon gazawar da suka yi wajen dakile karuwar miyagun laifuka a karamar hukumar.

An tare Matasan ne yayin da suke komawa Fatakwal daga sansanin masu yi wa kasa hidima (NYSC) da ke jihar Ondo, yayin da wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton masu garkuwa da mutane ne suka yi awon gaba da motar bas din su a yankin Emohua dake kan titin Gabashi zuwa Yammaci a daren ranar Talata.

Jami’ar hulda da jama’a ta rundunar ‘yansanda (PPRO) a jihar, Grace Iringe-Koko, ta shaida wa manema labarai a Fatakwal cewa wasu daga cikin ‘yan hidimar kasar sun kubuta daga hannun ‘yan ta’addan.

Iringe-Koko ta bayyana cewa, an tura kwararru zuwa yankin domin tabbatar da ganin an kubutar da ‘yan hidimar kasar da aka sace.

Sai dai ba ta bayyana adadin wadanda suka tsira ba da kuma adadin wadanda aka yi garkuwa da su.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Next Post
Montana Ta Zama Jihar Amurka Ta Farko Da Ta Haramta TikTok

Montana Ta Zama Jihar Amurka Ta Farko Da Ta Haramta TikTok

LABARAI MASU NASABA

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version