Dalilin Da Ya Sa Za A Yi Wa Tsohuwar Ministar Jin Ƙai Titsiye Kan Biliyan ₦729
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Ya Sa Za a Yi Wa Tsohuwar Ministar Jin Ƙai Titsiye Kan Biliyan ₦729

byAbubakar Sulaiman
1 year ago
Tsohuwa

Babbar Kotun Tarayya a Legas, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Deinde Dipeolu, ta umurci tsohuwar Ministar Harkokin jin ƙai Hajiya Sadia Umar-Farouk, da ta bayyana cikakkun bayanai na yadda aka rarraba N729 biliyan ga ‘yan Najeriya miliyan 24.3 cikin watanni shida. Wannan hukuncin ya zo ne sakamakon ƙarar ƴancin samun bayanai da ƙungiyar SERAP ta shigar.

A cikin hukuncinsa, Mai Shari’a Dipeolu ya umurci tsohuwar ministar da ta bayar da jerin sunayen waɗanda suka ci gajiyar kuɗaɗen, yawan jihohin da suka samu tallafin, da kuma yadda aka rarraba kuɗaɗen a kowace jiha.

Ya kuma umurci Hajiya Umar-Farouk da ta bayyana sharuɗɗan da aka yi amfani da su wajen zaɓen waɗanda suka ci gajiyar kuɗaɗen da kuma hanyoyin biyan kuɗin. Kotun ta nemi ƙarin bayani kan yadda aka ware ₦5,000 ga kowanne Mutum daga cikin mutanen miliyan 24.3, wanda ke wakiltar kashi biyar cikin ɗari na kasafin kuɗin Najeriya na 2021 wanda ya kai Naira tiriliyan #13.6t.

  • SERAP  Ta Nemi Majalisa Ta Yi Watsi Da Bukatar Gina Wa Shettima Gidan Naira Biliyan 15
  • Sojoji Sun Kashe Kasurgumin Dan Bindiga, Buharin Yadi

Mai Shari’a Dipeolu ya yi watsi da hujjojin da lauyan tsohuwar ministar ya gabatar, ya jaddada cewa ƙin bayyana bayanan da ake nema ba shi da uzuri. Ya ƙara da cewa rashin bin dokokin da kotun ta shinfiɗa za a ɗauke shi a matsayin bijirewa.

Yayin da yake mayar da martani kan neman a soke tuhumar ministar, Mai Shari’a Dipeolu ya yi nuni da buƙatar doka ta cewa dole ne hukumomin gwamnati su amsa buƙatun bayanai cikin kwanaki bakwai, kamar yadda dokar ‘Yancin Samun Bayanai ta tanada ta FOI.

Ya kammala da cewa ƙarar da SERAP ta shigar ta bi ƙa’ida cikin lokacin da ya dace, don haka ya yi watsi da ikirarin cewa an shigar da ƙarar bayan ta sauka daga minista.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Next Post
Li Qiang Ya Taya Keir Starmer Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Birtaniya

Li Qiang Ya Taya Keir Starmer Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Birtaniya

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version