Abubakar Abba">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home NOMA

Dalilinmu Na Tallafa Wa Masu Sana’ar Kifi A Legas – Daraktan BATNF

by Abubakar Abba
December 17, 2020
in NOMA
2 min read
Sana’ar Kifi
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

A ci gaba da goyon bayansa ga kananan manoma dake a kasar nan kamfanin dake sarrafa Sigari (BATNF) ya tallafa masu sana’ar sayar da Kifi dake a jihar Legas da kayan gasa Kifi na zamani kyauta.

Da ya ke jawabi a wurin mika kayan na tallafin ga yan kasuwar a lokacin taron da ya gudana a Hukumar Kula da Aikin Gona ta jihar Legas (LSADA) dake a yankin a Oko Oba a anguwar Agege Legas, Daraktan Cibiyar Uwargida Abimbola Okoya, ta bukaci masu cin gajiyar su yi amfani da kayan aiki don canza rayuwarsu.

samndaads

Daraktan Cibiyar Uwargida Abimbola Okoya, ta ce, a tsawon lokaci, cikin goyon bayan da muke baiwa manoma, mun lura cewa ban da koyar da su kyawawan ayyukan gona akwai kuma bukatar samar da ingantaccen kifi kuma yana da mahimmanci a yi abubuwa uku.

A cewar Daraktan Cibiyar Uwargida Abimbola Okoya, na daya akwai koya musu hanyoyin samun ingantaccen Kidi da fitar dashi da samar masu da kasuwa da kara karfafa musu gwiwa don kara darajar sana’ar tasu.

Daraktar Cibiyar Uwargida Abimbola Okoya, ta sanarda cewa, wannan tallafni da horarwa kan kyawawan ayyuka a cikin kifin da sarrafawa da kuma shirya su, muna fatan kasuwancinku da kudin shiga mai ya wa a karshe zaku fara fitarwa zuwa kasashe na ciki da wajen yankin Afirka.

A wata sabuwa kuwa, Kwamishinan ma’aikatar gandun daji na jihar Ogun Mista Kolawole Lawal ya sanar da cewa, za’a fara aikin noman gandun daji da farfado da kawata daji a jihar.

Ya sanar da hakan ne ga manema labarai hakan a garin Abeokuta, inda ya ce, manufar aikin, ita ce don a samar da ayyukan yi musamman a tsakanin dimbin matasan dake jihar.

Idan za a iya tunawa a kwanan baya, Kwamishinan ma’aikatar gandun daji na jihar Mista Kolawole Lawal, a ofis dinsa ya gudanar da tattaunawa a da wanda ke lura da shirin Mista Pierre Decroid.

A cewar Kwamishinan na ma’aikatar gandun daji na jihar Mista Kolawole Lawal, gwamnatin jihar za ta kuma wayar da kan alumomin da ke zaune a yankunan da za a gudanar da aikin, musamman gannin alfanun da aikin yake dashi ga raywar su, ya kara da cewa, aikin zai amfani alumomin da ke yankin da zama ganin cewar ta hanyar aikin za su samu dimbin ayyukan yi harda dimbin matasan da ke zaune a yankuna, inda ya kara da cewa, baya ga hakan, aikin zai taimaka matuka wajen yakar dumamar yanayi da kuma kara samar da abinci mai yawa a jihar.

Kamfanin dillancin labarai na kasa a kwanan baya ya ruwaito Gwamnan jihar ta Ogun Ibikunle Amosun ya jagoranci wata tawagar kula da dumamar yanayi data zo jihar daga Majalisar Dinkin Duniya, inda kuma tawagar, ta yi amfani da damar zuwa jihar, inda tawagar ta tattauna da jami’an kamfanin Lafarge Holcim da sauran masu zuba jari kan aikin farfado da kawata gandun.

Decroid ya jinjina wa gwamnatin jihar kan samar da wannan shirin, inda ya yi nuni da cewa, aikin zai zamo abin alfahari ga kowa, indan an kammala shi.

SendShareTweetShare
Previous Post

Yadda Za A Rage Karancin Abinci A Nijeriya Daga Kwararre

Next Post

Majalisar Dattawa Za Ta Amince Da Kasafin 2021 Ranar Litinin

RelatedPosts

Noman Kashu Na Taimaka Wa Fannin Tattalin Arziki, Cewar NCAN

Noman Kashu Na Taimaka Wa Fannin Tattalin Arziki, Cewar NCAN

by Abubakar Abba
4 hours ago
0

kungiyar masu noman Kashu ta kasa (NCAN) ta yi kira...

Shirin Aikin Noma Na LIFE-ND Zai Inganta Rayuwar Mazauna Yankin Neja-Delta – Minista

Shirin Aikin Noma Na LIFE-ND Zai Inganta Rayuwar Mazauna Yankin Neja-Delta – Minista

by Abubakar Abba
4 hours ago
0

Gwamnatin Tarayya ta sanar da cewa, za ta kashe akalla...

Dalilinmu Na Noma Tumbar Kadada 15,000 Na Roba A Kuros Ribas – NARPPMAN

Dalilinmu Na Noma Tumbar Kadada 15,000 Na Roba A Kuros Ribas – NARPPMAN

by Abubakar Abba
4 hours ago
0

Akwai alamun dake nuna cewa, akwai fata nagari a fannin...

Next Post
Kasafin 2021

Majalisar Dattawa Za Ta Amince Da Kasafin 2021 Ranar Litinin

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version