Daminar Bana: Gwamnan Gombe Ya Kaddamar Da Sayar Da Taki Mai Rahusa
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daminar Bana: Gwamnan Gombe Ya Kaddamar Da Sayar Da Taki Mai Rahusa

byKhalid Idris Doya
2 years ago
Gombe

Gwamnan Muhammadu Inuwa Yahaya na Jihar Gombe, ya kaddamar da sayar da takin zamani na daminar bana da nufin bunkasa noma a jihar.

Da yake kaddamar da takin a gidan gona na Lawanti da ke karamar hukumar Akko, gwamnan ya ce za a sayar da takin ne kan kudi Naira 19,000 kan kowane buhu, sabanin farashin kasuwa da ya kai kusan Naira 26,000, don samarwa manoman jihar sauki.

  • EFCC Ta Sallami Ortom Bayan Tsare Shi Na Tsawon Sa’o’i
  • Gamayyar Masu Ruwa Da Tsaki A Harkar Ilimi Sun Goyi Bayan Gwamnatin Kano Na Kwato Filayen Makarantu

Gwamnan ya ce, “Gwamnati ta sayo tirela 160 na takin kan kudi Naira biliyan biyu da miliyan dari takwas da talatin, karin kimanin tireloli 35 kenan a kan na bara.”

Don tabbatar da cewa takin ya kai ga ainihin manoma, Gwamna Inuwa ya bayyana cewa gwamnatinsa ta samar da ingantaccen tsarin sayar da shi a dukkan gundumomin jihar 114 don tabbatar da cewa takin ya kai ga manoma na hakika tun daga tushe.

“Mun fahimci cewa tsadar taki da sauran kayayyakin amfanin gona na iya zama babban cikas ga manomanmu, don haka ne muke aiki tukuru wajen samar da wannan taki a farashi mai rahusa don ragewa manomanmu dawainiyar kudi.

“Burinmu shi ne mu tallafa musu da muhimman kayan aikin noma don bunkasa amfanin gona da inganta kasa, da habaka ribar da suke samu, da kuma tabbatar da dorewar harkokin noma a jiharmu”.

Gwamnan ya ce gwamnatinsa ta gudanar da ayyuka da shirye-shirye daban-daban na inganta harkar noma a Gombe, don haka jihar ta shiga cikin harkoki da tsare-tsaren noma da dama a matakin jiha da shiyya da kuma kasa baki daya don bunkasa harkar ta noma.

“Gwamnati ta kuma samar da shirin tallafi na ‘NG-cares’ don samar da taki da sinadaran noma ga manomanmu kyauta, mun kuma hada gwiwa da ma’aikatar noma da raya karkara ta tarayya wajen horar da manoma kan noman masara da doya, inda aka bai wa wadanda suka amfana kayan aikin da suka dace don nomansu.”

Sai ya yi kira ga manoman su bai wa wadanda aka dorawa alhakin sayar da takin da rarraba shi a fadin jihar hadin kai don samun nasarar aikin.

Ya kuma gargade su, da su guji karkatar da takin.

Ya kara da cewa Jihar Gombe jiha ce ta noma, inda fiye da kaso 80 cikin dari na al’ummarta manoma ne, “Saboda haka tallafawa wannan bangare yana da matukar muhimmanci ga ci gaban tattalin arziki, da samar da abinci, da dorewar rayuwar jama’armu”.

Tun farko a jawabinsa na maraba, Daraktan Tsare-Tsare, Bincike da Kididdiga a Ma’aikatar Noma da Kiwo, Dakta Ibrahim Yakubu Usman, ya ce, an kafa kwamitocin yaki da rikicin makiyaya da manoma don magance rikice-rikice da allurar rigakafin cututtukan dabbobi masu yaduwa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
Kroos Ya Kara Kwantiragin Shekara 1 A Real Madrid

Kroos Ya Kara Kwantiragin Shekara 1 A Real Madrid

LABARAI MASU NASABA

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version