Daminar Bana: Manoma A Nijerya Na Cikin Fargabar Ambaliyar Ruwa
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daminar Bana: Manoma A Nijerya Na Cikin Fargabar Ambaliyar Ruwa

byAbubakar Abba
3 years ago
Manoma

Manoma a jihohi daban-daban a kaar nan, na cikin fargabar aukuwar ambaliyar ruwan da za ta iya kwarara zuwa cikin gonakinsu.

Wasu daga cikin jihohin sun hada da Kebbi da Bauchi da Zamfara da Sakkwato da Kwara da Ribas da Kuros Riba da sauransu.

  • Kananan Manoma 31,666 Sun Samu Tallafin Noma Naira Biliyan 5.9 – CBN

Tuni dai, hukumar kula da yanayin ruwa ta kasa ta sanar da cewa, ruwan da ya taru a Kogin Neja zai iya zama babbar barazana ga gonakan manoma, musamman wadanda ke jihohin Kebbi da Neja da Kwara da Nasarawa da Kogi da Anambra da Delta da Edo da Ribas da kuma Bayelsa wadanda kogin ya ke ta su.

Bugu da kari, Darakta-Janar na hukumar kula da yanayin ruwa ta kasa, Mista Clement Onyeaso Nze a wani rahoton ta ya fitar, ya yi hasashen cewar za a fara samun ambaliya a kasar nan daga 6 ga watan Satumba a Jihar Kebbi.

Alalmisali, a daminar bara ambaliya ta jawo wa dubban manoma wadanda akasarinsu manoman shinkafa da masara ne a jihohin Kebbi da Bauchi da Zamfara da Sakkwato, da Kwara da Ribas da Kuros Riba da sauransu, babbar asara.
Masana a fannin aikin noma a kasar nan, sun bayyana cewa, ambaliyar za ta jawo karancin abinci a a kasar nan, inda hakan zai kuma haifar da hauhawar farashin kayan abinci.

Har ila yau, sakamakon ambaliyar ruwan da ta auku a daminar bara, ta jawo tashin farashin kayan abinci, misali, sai da farashin buhun masara a jihar Kano ya kai naira 20,000.

Bugu da kari, a jihar Binuwai kuwa, farashin ya kai naira 22,000; a birnin tarayar Abuja kuwa ya kai naira 24,000, inda a jihar Legas ta kai naira 25,000.

Lamarin na tashin farashin sakamokon aukuwar ta ambaliyar ruwa, sai da ya shafi farashin shinkafar da ake noma wa kasar nan, inda buhunta ya kai naira 55,000 a Abuja ya kai naira 58,000.

Wani masani a fanin samar da abinci ya sanar da cewa, kasar nan za ta iya aukawa a cikin matsalar karancin abinci.
Bugu da kari, a shekarar da ta gabata Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Jihar Kebbi ta sanar da cewa, sakamakon ambaliar da ta auku a bara, ta lalata kimain kadada 450,000 na gonakin shinkafa tare da lalata kadada 50,000.

Bisa hasashen da aka yi, manoma a jihar ta Kebbi sun tabka asarar da ta kai ta sama da naira biliyan biyar.
Wani manomin shinkafa a jihar ta Kebbi Garba Bala ya bayyana cewa, sakamakon ambaiyar ta bara ya yi asarar kimain kadada 16,000.

Ya kara da cewa, ya samo rancen ne daga banki don ya kara habaka nomansa na shinkafar wasu kuma daga cikin manoman shinkafar da iftila’in na ambaliyar ruwan ta aukawa gonakan su da suka shuka shinkafar sun bayyana cewa, samo rance ne a karkashin shirin aikin ma na gwamnatin tarayya na Anchor Borrowers da ke karkashin kulawar babban bankin Nijeriya.

Shi ma wani manomin shinkafa a jihar Sani Muhammad ya ce, ambaliayar ta lalata masa kadada shida tare da wasu kadada da ya shuka masara.

An ruwaito Shugaba kungiyar manoma ta kasa Ibrahim Kabiru ya ce ambaliyar ta fi shafar gonakin shinkafa da dawa da sauran amfanin gona.

Kabiru ya kara da cewa, zai yi wuya a iya iyakance barnar da ambaliya ta haifar a gonakan manoman, inda ya bayyana cewa, a gefe guda kuma manoma a kasar, musamman a arewacin kasar nan na ci gaba da fuskantar barazanar rashin tsaro saboda hare-haren ‘yan bindiga, inda hakan ya tilasta wa maona da dama, kaurace wa gonakinsu don gudun kar masu garkuwa su sace su ko kuma su hallaka su a yayin da suka je gonakarsu don yin noma.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

October 3, 2025
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

October 3, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

September 27, 2025
Next Post
Peter Obi Ya Jajantawa Ekweremadu Kan Cafke Shi Da Aka Yi a Burtaniya

Peter Obi Ya Jajantawa Ekweremadu Kan Cafke Shi Da Aka Yi a Burtaniya

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version