Dan Majalisa Ya Kaddamar Da Ajujuwa 3 A Firamare A Adamawa
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dan Majalisa Ya Kaddamar Da Ajujuwa 3 A Firamare A Adamawa

byMuh'd Shafi'u Saleh
1 year ago
Dan Majalisa

Dan majalisar wakilai mai wakiltar kananan hukumomin Numan/Demsa/Lamurde, Honarabul Kwamoti La’ori, ya kaddamar da ginin ajujuwan karatu uku, a makarantar firamare da ke garin Kwah a karamar hukumar Lamurde a jihar Adamawa.

Da yake jawabi a taron dan majalisa Kwamoti La’ori, ya gode wa Allah da ya ba shi damar cika alkawarin da ya yi wa jama’a lokacin yaƙin neman zaben ya ce ba iyawarsa ba ne, ya yi alkawarin ci gaba da yi wa jama’a hidima.

  • Hungary Na Sa Ran Ziyarar Xi Za Ta Bude Sabon Babi A Dangantakarta Da Sin
  • NNPCL Ya Bayyana Ranar Da Matatar Man Fetur Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki

La’ori ya kuma bukaci jama’a da su ci gaba da bai wa tsare-tsaren gwamna Ahamdu Umaru Fintiri, goyon baya domin tabbatar da samun zaman lafiya “idan kun samu bayanai ku sanar da gwamnati domin daukan mataki a kan lokaci”.

Ya kuma yi alkawarin isar da sakon gudanar da aikin babbar hanyar kamar yadda jama’ar yankin suka bukata ga hukumomin da suka dace.

Da ita ma ke jawabi shugabar malamai na makarantar Salome Nicoderius, ta nuna matukar farin ciki da jinjina wa dan majalisar bisa aikin gina ajujuwan da ya yi, ta kuma koka da karancin malamai a makarantar.

A nasa jawabin, tsohon shugaban karamar hukumar Lamurde Bulus Daniel, ya bayyana siyasar fada da cewar dan majalisar da cewa abu ne da ya kamata a ce ‘yan siyasa sun koya.

Ya ce “idan mu ‘yan siyasa za mu yi koyi da irin siyasarka to kuwa za mu cimma nasara, ni da kan ne fitilar siyasa na, zan ci gaba da koyi da kai” in ji Bulus.

Da shi ma ke jawabi sarkin Kwah Mista Nickson Tamuna, ya bayyana dan majalisar a matsayin babban alfahari da kyautar da Allah ya yi wa jama’ar yankin da jihar Adamawa, ya kara da cewa “ka zo mana da alherin da ba zamu taba mantawa da shi ba, muna neman da kayi amfani matsayinka na ganin an gyara mana babban hanyar Lamurde zuwa Karim” in ji sarkin.

Baya ga karrama dan majalisa Kwamoti La’ori da mukamin (Inuwar Kwah), an kuma gudanar da rawar gargajiya na kabilun yankin a lokacin taron na jiya Litinin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
Shugaban Serbia: Zan Rubuta Wani Littafi Don Tunawa Da Hulda Ta Da Xi Jinping

Shugaban Serbia: Zan Rubuta Wani Littafi Don Tunawa Da Hulda Ta Da Xi Jinping

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version