Dan Takarar Gwamnan PDP Ya Nemi Goyon Bayan Ma'aikata A Kaduna
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dan Takarar Gwamnan PDP Ya Nemi Goyon Bayan Ma’aikata A Kaduna

byIdris Umar
3 years ago
PDP

Dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP a Jihar Kaduna, Honorabul Isa Ashiru Kudan, ya kai ziyarar tare da neman goyan baya ga Malamai da Ma’aikatan Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya (ABU), kan kudurinsa na neman kujerar gwamnan jihar a zabe mai zuwa.

An gudanar da taron a babban dakin taro da ke Cibiyar Aikin Gona na jami’ar.

  • Tinubu Ne Kadai Zai Iya Magance Rashin Tsaro Da Tabarbarewar Tattalin Arziki – Buhari 
  • Babu Gaskiya A Labarin Cewar G-5 Ta Goyi Bayan Takarar Atiku – Samuel Ortom

Taron ya samu halartar manyan Farfesoshi, Daktoci da sauran masu ruwa da tsaki a jihar.

Shugaban taron, Dakta Hamisu Lawal, ya ce dan takarar nasu na neman goyon bayan jama’a a matsayinsa na mai son ya jagoraci al’umar Jihar Kaduna.

Shugaban ya kara da cewa ma’aikatan Suna son kuma su mika tambayoyin da suka shafi kujerar da yake nema don samun fahimtar juna tare da shifida tafiya mai tsafta a tsakanin al’umar dake jihar Kaduna baki daya.

Farfesoshi ne da manyan yan Boko da gogaggun yan siyasa suka halacci wannan taro

Honorabul Isa Ashiru ya saurari tambayoyi daga mahalatta taron wanda suka shafi kudirin da ke kare mutuncin al’umma kamar maganar kalubalen da harkar Ilmi ke fuskanta a halin yanzu, da kuma maganar tabarbarewar da harkar tsaro dake kara girma a halin yanzu sai maganar jin dadi da walwalar ma’aikata da komi ya lalace a jihar ta Kaduna.

Hakazalika, ya ce Ashiru ba shi da wani buri face sauya fasalin jihar, ta hanyar shimfida ayyukan more rayuwa da jina al’umma.

A nasa jawabin, shugaban jam’iyyar PDP a Jihar Kaduna, godiya ya yi ga dubban ma’aikatan jami’ar bisa yadda suka nuna kauna ga dan takarar nasu, inda ya ce da ikon Allah PDP ba za ta bai wa jama’a kunya ba.

Dan takarar gwamnan na PDP, Ashiru, ya bayyana jib dadinsa kan yadda ma’aikatarln suka yi masa dafifi don nuna goyon bayan takararsa.

“Na ji dadi sosai kuma na samu kwarin guiwa a tafiyarmu a jiha da kasa baki daya.”

Ashiru na PDP zai kara da Sanata Uba Sani na jam’iyyar APC mai mulki a zaben gwamnan jihar da za a gudanar a ranar 11 ga watan Maris, 2023.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas
Labarai

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

October 2, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

September 28, 2025
Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas
Siyasa

Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas

September 27, 2025
Next Post
Kananan Yara Fiye Da Miliyan 5 Sun Mutu A 2021- Majalisar Dinkin Duniya

Kananan Yara Fiye Da Miliyan 5 Sun Mutu A 2021- Majalisar Dinkin Duniya

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version