Dan Takarar Gwamnan ZLP A Bauchi Ya Musanta Janye Takararsa
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dan Takarar Gwamnan ZLP A Bauchi Ya Musanta Janye Takararsa

byKhalid Idris Doya
3 years ago
ZLP

Jam’iyyar ZLP a Jihar Bauchi, ta bukaci babban lauya, Eko Ejembi (SAN) da abokan aikinsa da su fara shirye-shiryen daukar matakan shari’a kan kwamitin yakin zaben shugaban kasa na jam’iyyar PDP bisa bayyana cewa dan takarar jam’iyyar a Jihar Bauchi, Ambasada Khalid Arewa ya koma PDP tare da janye takararsa.

Idan ba a manta ba a ranar Talata kwamitin yakin zaben shugaban kasa na jam’iyyar PDP, ya ziyarci Jihar Bauchi domin yakin zabensa, inda kusoshi na jam’iyyar ciki har da dan takarar shugaban kasa, Atiku Abubakar da gwamna Bala Muhammad suka halarta, inda aka bayyana sunayen wasu da suka koma PDP ciki har da ayyana sunan dan takarar gwamna na jam’iyyar ZLP.

  • Ya Kamata Amurka Ta Sauya Mahangar Ta Game Da Sin
  • Na Yi Alkawari Zan Kawar Da Matsalolin Al’umma, In Ji Tinubu

A hirarsa da LEADERSHIP Hausa a ranar Alhamis, dan takarar, ya karyata labarin, ya kuma nuna bacin ransa tare da cewa kwata-kwata babu wanda ya tuntubesa kan wannan zance.

“Ina zaune a ofis ina ganawa da wasu sai aka fara kirana a waya ana tambayata, ya aka yi aka ji sunana cewa na koma PDP?

“Na ce ban gane ba, wace magana ce wannan?. Wasa gaske na amsa kiran waya kan wannan batun a lokacin sama da 100, inda magoya bayanmu suna nuna takaicinsu da nuna bacin ransu da jin wannan maganar.

“Gaskiya ni ban san da wannan batu ba kuma ba a yi wannan zancen da ni ba. Kuma ba mu shirya cewa zan sauya sheka na koma wata jam’iyya ba.

“Kowa ya ga yadda muka karbu a Jihar Bauchi, babu wani matashi kamata a duk ‘yan takarar nan, ni ne mai karancin shekaru kuma matasa suna alfahari da hakan. Sun kuma shirya wajen ganin nasu ya karbi mulki. Alhamdullahi muna kallon nasara domin tsakaninmu idan har aka yi zabe bisa gaskiya to ni zan ci, sai dai idan magudi za a yi.”

Ya ce, ya fito ya barranta kansa da wannan ikirarin da PDP da ‘yan takaranta suka yi a gaban dubban jama’a.

“Na rubuta wasika zuwa ga babban lauya na kasa kuma muna jiran amsarsa, domin ka san mai neman shugaban kasa zan yi kara Atiku Abubakar da Dino Melaye da ya kira sunana, da kuma shugaban jam’iyyar PDP na kasa Iyorchia Ayu, da shugaban PDP na Jihar Bauchi, Hamza Koshe Akuyam.”

Arewa, ya sha alwashin samun nasara a zaben gwamna na 11 ga watan Maris, 2023.

“Wannan bata suna ne baro-baro a matsayina na dan takarar gwamna da nake kallon zan ci zabe, yanzu a sakamakon wannan furucin da suka yi na rasa akalla kashi 30 na magoya bayana.

“Wani daga jin wannan batun shi ke nan ya tafi da shi a ransa ke nan, wani kuma zai ga tun farko yaudararsa aka yi, wani kuma zai ga ban kyauta wa masoyana ba, kowa da yadda zai dauki batun, don haka ba lamari ne da za mu bar shi haka nan ba.”

Arewa ya ce, kwata-kwata babu wata yarjejeniya da suka yi da gwamnatin Jihar Bauchi ko PDP kan cewa zai janye takararsa ba.

“Idan ma za mu janye ya kamata a ji nunfashinmu balle ma hakan baya daga cikin manufarmu. Shin an ma fito an fadi hakan a kan mu don an fi mu cancanta ne ko don rainin da aka mana? Ko kuma a’a fahimtarmu ce ta zo daya, amma babu haka kawai mutum ya tashi kawai ya ce mun janye neman takararmu hakan ba za ta yiwuwa ba.”

A kwafin wasikar da ZLP ta aike wa Lauyoyin ta ce, “Daukan matakin shari’ar shi ne zai dawo wa jam’iyyarmu da kima da mutuncinta kan yarfen da aka mana.”

Wasikar mai dauke da sanya hannun Ambasada Khalid Arewa, dan takarar gwamna na jam’iyyar, “Kwasam a ranar 7 ga watan Fabrairu, 2023 PDP-PCC ya kira sunan dan takarar gwamnanmu a jihar Bauchi, Ambasada Khalid Arewa da cewa ya koma jam’iyyar PDP, wannan furucin ya janyo mana asara sosai da jawo damuwa.”

“Tun lokacin da PDP ta fito ta yi wannan furucin, magoya baya da masoyan ZLP sun shiga damuwa sun kuma nuna rashin jin dadinsu a sassa daban-daban na kananan hukumomin jihar Bauchi.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas
Labarai

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

October 2, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

September 28, 2025
Next Post
Sin Ta Ba Da Agajin Kayayyakin Aikin Jinya Ga Syria

Sin Ta Ba Da Agajin Kayayyakin Aikin Jinya Ga Syria

LABARAI MASU NASABA

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version