Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Dana Ya Na Nan A Raye – Tijjani Asase

by
3 years ago
in KANNYWOOD
2 min read
Dana Ya Na Nan A Raye – Tijjani Asase
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Kamar yadda wasu kafafen yada labarai ke ta faman yada farfaganda cewa, an hallaka dan fitaccen Dan wasan Kwaikwayon nan, Tijjani Asase, wanda bai jima da kammala saukar Alkur’aninsa ba, ta hanyar kwace ma sa keken Adaidaita Sahu a jihar Kano, wannan ba gaskiya ba ne, illa shaci fadi kawai.

Mun samu wannan sanarwa ne daga shafin sadar da zumunta na daya daga cikin makusantan Tijjani Asasen, wato Mudassir Kasim, inda ya bayyana cewa, ya tuntubi Asasen don jin gaskiyar al’amarin dangane da wannan abin da ke faruwa, ya kuma yi ma sa bayani daki-daki kamar haka:

“Na bayar da cigiyar Babur din Adaidaita Sahu, wanda a ka sace wa wani dan’uwana, wanda yake kamar Da a wurina. A wajen bayar da wannan sanarwa, ko kadan ban ambaci sunan dana wanda ya yi saukar Alkur’ani a kwanakin baya ko wani abu mai kama da haka ba, amma kawai ni ma sai ji na yi na kuma gani a shafukan sada zumunta na Facebook, a na ta faman yada wannan farfaganda wadda ko kadan ba ta da asali ballantana tushe.”

Labarai Masu Nasaba

Dalilan Da Suka Janyo Rabuwar Aurenmu Da Jaruma Fati Muhammad —Mai Iska

Na Hadu Da Mutanen Kirki Da Mutanen Banza A Harkar Fim -Nadiya Adamu

Babban abin haushi da takaicin ma shi ne, yadda wasu Kafafen yada labarai wadanda mafiya yawansu al’umma na girmama labaransu tare da ba su muhimmaci, amma sai ga shi su ma sun buge da yayata irin wadannan labarai marasa tushe da kuma kan-gado kwata-kwata.

A karshe, Kasim ya ja hankali tare da baiwa irin wadannan kafafen yada labarai irin na kanzon kurege shawara musamman ta fuskar rika yin kokarin tantance labaran gaskiya kafin su kai ga fara yada shi a cikin al’umma ko irin wadannan kafafen yada labarai na zaurukan sadar da zumunta da sauran makamantansu, domin kuwa a cewar tasa, hakan babu abin da zai Haifa musu, illa zub da kima da kuma mutunci a idanun al’umma da kuma sauran wadanda ke saurare ko bibiyasu a irin wadannan zauruka.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Mandawari Ya Ci Albasa Da Bakin Kannywood: Ya Zayyana Wa Osinbajo Hanyoyin Bunkasa Masana’antar

Next Post

Ba Ma Koyar Da Tarbiyya, Cewar Yaron Adam Zango

Labarai Masu Nasaba

Dalilan Da Suka Janyo Rabuwar Aurenmu Da Jaruma Fati Muhammad —Mai Iska

Dalilan Da Suka Janyo Rabuwar Aurenmu Da Jaruma Fati Muhammad —Mai Iska

by
1 month ago
0

...

Fim

Na Hadu Da Mutanen Kirki Da Mutanen Banza A Harkar Fim -Nadiya Adamu

by
4 months ago
0

...

Kannywood

Matsalolin Masana’antar Fina-finan Hausa Da Ke Neman Kassara Ta

by
5 months ago
0

...

Mata

Fim Din ‘MATA DOZIN’ Ya Fito Da Matsalolin Da Mata Ke Fuskanta A Wannan Zamanin —Ibrahim Bala

by
6 months ago
0

...

Next Post

Ba Ma Koyar Da Tarbiyya, Cewar Yaron Adam Zango

Leave Comment

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: