Dangote Ya Bada Shawarar Samar Da Gidaje Masu Rahusa Da 'Yan Nijeriya Za Su Iya Mallaka
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dangote Ya Bada Shawarar Samar Da Gidaje Masu Rahusa Da ‘Yan Nijeriya Za Su Iya Mallaka

bySulaiman
2 months ago
Dangote

Kamfanin Siminti na Dangote ya bukaci masu ruwa da tsaki a harkar samar da gidaje da su yi la’akari da tsarin samar da gidaje ga ‘yan Nijeriya da ya dace da daidai kasafin kudin masu karamin karfi.

 

Da yake jawabi a wajen bikin baje kolin gidaje na kasa da kasa na Afirka, Daraktan tallace-tallace na Kamfanin Siminti na Dangote, Dolapo Alli, ya ce: “Maganin matsalolin gidaje na bukatar hadin gwiwa tsakanin masu ruwa da tsaki, da suka hada da hukumomin gwamnati, masu zaman kansu, da al’ummomi. Gwamnati za ta iya rungumar tsarin hadin gwiwa da kamfanoni masu zaman kansu don samar da gidaje masu rahusa ga al’umma wanda aka fi sani da shirin PPP.

  • Zargin Da Wasu ’Yan Siyasar Amurka Ke Yi Wa Sin Na Fitar Da Hajoji Fiye Da Kima Ya Sabawa Hujjoji Na Hakika
  • Kamfanonin Sadarwa Za Su Ci Gaba Da Rajistar Sabon SIM – NIMC

“Ta hanyar tsarin PPP, gwamnati na iya ƙaddamar da gina sabbin gidaje, yayin da kamfanoni masu zaman kansu dake masana’antar gine-gine kuma a saukake musu haraji tare da basu lamuni don saukake samar da kudade na sababbin gidaje masu rahusa.”

 

Mista Alli, wanda yake jawabi a rana ta musamman ta kamfanin, ya ce, samar da gidaje masu yawa na daya daga cikin dabaru da dama da ake amfani da su wajen magance kalubalen karancin gidaje ga jama’a, inda ya kara da cewa, amma wannan tsarin ya taimaka wajen magance matsalolin da ke tattare da saurin bunkasar birane a kasashe da dama na duniya.

 

Ya yabawa kokarin Gwamnatin Tarayya wajen aiwatar da shirye-shiryen samar da gidaje masu yawa, inda ya kara da cewa, amma akwai bukatar a cike gibi.

 

Ya ce: “Nijeriya, ta hanyar shirin sabunta fata na samar da gidaje da gwamnatin shugaba Tinubu ta kirkiro, ta dauki matakan yabawa wajen magance babban gibin da ke tattare da samun lamunin kudade wajen samar da gidaje masu rahusa. Wannan shiri na nuni da cewa, an himmatu wajen ganin ‘yan kasa sun samu saukin mallakar gidaje, musamman masu karamin karfi da matsakaita tattalin arziki.

 

Ya bukaci gwamnatoci a dukkan matakai da su aiwatar da ingantattun tsare-tsare tare da samar da filayen gina gidaje masu tarin yawa a Nijeriya.

 

Kamfanin Siminti na Dangote na daya daga cikin masu daukar nauyin shirin baje kolin gidaje na Afirka (AIHS) wanda za a rufe ranar Juma’a 1 ga Agusta, 2025.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Next Post
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafi Jawabin Xi Jinping Game Da Kiyaye Muhallin Halittu

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafi Jawabin Xi Jinping Game Da Kiyaye Muhallin Halittu

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version