Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home JAKAR MAGORI

Direba Ya Gane Wanda Ya Taba Garkuwa Da Shi Cikin Fasinjojin Motarsa A Sokoto

by Muhammad
December 2, 2020
in JAKAR MAGORI
2 min read
Motarsa
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Wani direban motar daukar fasinja ya gane wani mutum da ya taba yin garkuwa da shi daga cikin fasinjojin da ya dauka a motarsa a tashar Kwannawa da ke Jihar Sokoto. Direban wanda aka yi garkuwa da shi watanni biyu da suka gabata a Karamar Hukumar Kankara da ke Jihar Katsina ya yi saurin gane mutumin kuma ya sanarwa da shugabbanin tashar.

‘Yan sanda sun kama wanda ake zargin kuma tuni aka mai da al’amarin zuwa hedikwatar ‘yan sanda ta Sokoto don fadada bincike. Wannan lamari ya faru a tashar mota ta Kwannawa da ke Karamar Hukumar Dange-Shuni a Jihar Sokoto, bayan da wannan direba ya shaida wanda ya taba yin garkuwa da shi a cikin fasinjojin da ya dauka a cikin motarsa.

samndaads

Direban wanda aka sakaya sunansa, an yi garkuwa da shi a Kankara da ke Jihar Katsina watanni biyu da suka gabata. Majiyarmu ta ruwaito cewa direban ya shafe kimanin sati uku a tsare a wurin masu garkuwar bayan biyan kudin fansar da ba’a bayyana adadinsu ba.

Wanda ake zargin ya gamu da cikas, lokacin da ya shiga mota zuwa Kano, ba tare da sanin ita ce motar da suka tare suka yi garkuwa da direba ba. “Direban ya yi saurin gane shi saboda abin bai dade da faruwa ba. “Bayan gane shi, ya yi gaggawar sanar da Shugabannin kungiya su kuma suka sanar da ‘yan sanda mafi kusa,” wani dan kungiyar direbobi NURTW ya shaidawa manema labarai. Shugabannin kungiyar sun canja direban motar da wani bayan motar ta cika da fasinja kuma ya nufi garin Shuni. An ruwaito cewa a nan ‘yan sanda suka kama wanda ake zargin zuwa ofishinsu.

An mayar da wanda ake zargin zuwa hedikwatar ‘yan sanda ta Jihar Sokoto don fadada bincike. Mai magana da yawun rundunar, DSP Muhammad Sadik ya tabbatar da faruwar lamarin, kuma ya ce bincike su ke har yanzu.

SendShareTweetShare
Previous Post

An Cafke Fursunonin Da Suka Tsere Daga Kurkukun Edo A Kaduna

Next Post

Bikin Bajekoli Karo 41 Ya Kankama A Kano

RelatedPosts

‘Google Map’

Ya Tsunduma Motarsa Cikin Kogi Yayin Da Yake Bin Umarnin ‘Google Map’

by Sulaiman Ibrahim
7 hours ago
0

Wani ba indiye ya nitse bayan ya jefa motarsa a...

Suna Bauta Wa Saniyar Da Aka Haifa Da Kafa Biyar Don Kawo Masu Sa’a

Suna Bauta Wa Saniyar Da Aka Haifa Da Kafa Biyar Don Kawo Masu Sa’a

by Sulaiman Ibrahim
8 hours ago
0

Wani maraki da aka haifa da Kafa biyar ya zama...

Zakara

Zakara Ya Kashe Mutum A Yayin Fadan Zakaru

by Sulaiman Ibrahim
4 days ago
0

’Yan sanda sun bayyana cewa, a ranar Alhamis ne wani...

Next Post
Bajekoli

Bikin Bajekoli Karo 41 Ya Kankama A Kano

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version