Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home MANYAN LABARAI

Dokar Gwamnati: Ta Hana Likitocinta Aiki A Asibitin Kuɗi

by Tayo Adelaja
October 12, 2017
in MANYAN LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Ba Za Ta Biya Kwanakin Yajin Aiki Ba

Daga Sulaiman Bala Idris, Abuja

samndaads

Gwamnatin tarayya ta fara bin matakan hana likitocinta ci gaba da zuwa yin wasu ayyukan a asibitocin kuɗi. wanda wannan ba sabon abu bane a tsakankanin likitocin Nijeriya.

Bayanan waɗannan dokoki da ake ƙoƙarin zartaswa sun fito ne daga bakin Ministan Lafiya, Isaac Adeƙole, da takwaransa Ministan ayyuka, Chris Ngige. Waɗanda suka shaida wa manema labarai cewa wannan wani mataki ne da gwamnatin tarayya ta ɗauka a taron majalisar zartaswar da aka gudanar jiya.

A ta bakin gwamnatin, baya ga dokar daina biyan kwanakin yajin aiki, sannan akwai batun cewa a lokutan da ma’aikata za su kwashe suna yajin aiki ba za a ƙirga wannan kwanakin cikin kuɗaɗen fansho ɗinsu ba, kamar yadda Chris Ngige ya bayyana.

Ministan ya ce, wannan doka ce da tuntuni akwai ta a dokokin cinikayya, wanda kuma yayi kira ga ma’aikatu da ƙungiyoyin ƙwadago da su bibiyi dokokin don fahimtar yadda lamarin yake.

Ya ce; “Akwai lamurra da dama da muka tattauna su yau a zaman majalisar zartaswa. Dama kuma majalisar ta umurci Sakataren Fadar Gwamnati da ya samar da kwamitin da zai bibiyi lamuran ma’aikatan gwamnati. wannan kwamitin an samar da shi ne a ranar 27 ga watan Afrilun 2016.

“Wannan kwamitin an assasa shi ne ƙarƙashin jagorancin Sakataren Fadar Gwamnati, da taimakon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa. Daga cikin membobin kwamitin akwai Shugaban Biyan Albashi na Ƙasa, ma’aikatar ayyuka, ma’aikatar lafiya Ma’aikatar Kimiyya da Fasaha, ofishin atoni janar na ƙasa. Wannan rahoton da suka samar, a yau mun duba shi.

“Rahoton ya bayyana cewa a ƙaddamar da dokar da ke cewa ba za a biya ma’aikatan da suka tafi yajin aiki ba. Shi wannan wani doka ne da yake rubuce a dokar sasanci tsakanin ‘yan ƙwadago.” Inji Ngige

Minista Ngige ya ƙara da cewa, da ganin yanayin yadda ake tafiya yajin aiki a yanzu, ana yi ne domin a kawo cikas ga gwamnatin Buhari.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Sheikh Ɗahiru Bauchi Ya Musuluntar Da Aljani

Next Post

‘Yan Bindiga Daɗi Sun Kashe Tsohon Shugaban Ma’aikatan Filato

RelatedPosts

'Yan Adaidaita

An Sasanta Yajin Aikin ’Yan Adaidaita Bayan… Motocin ‘Kano Line’  Sun Koma Jigilar Jakara-Kasuwa

by Muhammad
1 day ago
0

Babu Hanunmu A Ciki Wannan Yaji – Shugaban ’Yan Adaidaita...

Adaidaita

Yajin Aikin Adaidaita: Acaba Ta Dawo A Kano

by Muhammad
2 days ago
0

Ya Jefa Jama’a Cikin Tsaka Mai Wuya Yadda Aka Koma...

Masu Garkuwa

Tattaunawa Da Masu Garkuwa: Yadda Gwamnonin Kaduna Da Neja Suka Raba Gari

by Muhammad
3 days ago
0

Shin Sheikh Gumi Ne Ya Raba Tsakani? Daga Nasir S....

Next Post

‘Yan Bindiga Daɗi Sun Kashe Tsohon Shugaban Ma’aikatan Filato

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version