DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

byAbubakar Sulaiman
1 month ago
Sowore

Hukumar tsaron farin kaya (DSS) ta ba ɗan gwagwarmayar dimokuraɗiyya kuma mawallafin Sahara Reporters, Omoyele Sowore, wa’adin mako guda domin ya janye wani abu da ya wallafa a shafin X (Twitter) kan Shugaba Bola Tinubu, wadda hukumar ta ce “ƙarya ce, ta ɓata suna kuma tana iya tada zaune tsaye.”

A cikin wasiƙar da DSS ta aika masa ranar 7 ga Satumba, 2025, ta zargi Sowore da yin kalaman batanci da cin mutunci ga shugaban ƙasa a wallafar da ya yi ranar 26 ga Agusta, inda ya kira Tinubu “ɓarawo” tare da zargin cewa ya yi wa ’yan Nijeriya ƙarya bayan ya ce cin hanci da rashawa sun daina wanzuwa a gwamnatinsa yayin da yake ziyara a Brazil. Hukumar ta yi gargaɗin cewa rashin bin umarninta zai tilasta mata ɗaukar duk wanivmataki na doka domin kare tsaron ƙasa da zaman lafiya.

  • Kotu Ta Bayar Da Belin Sowore Kan Naira Miliyan 10
  • Buratai Ya Bukaci Kotu Ta Ci Tarar Sowore Naira Biliyan 10 Kan Bata Masa Suna

DSS ta buƙaci Sowore da ya goge rubutun, ya sake wallafa sabuwar sanarwa a shafin X daidai da yadda ya bayyana tun farko, sannan ya buga sanarwar neman afuwa a aƙalla jaridu biyu na ƙasa da tashoshin talabijin biyu masu yaɗa shirye-shirye a faɗin ƙasa. Haka kuma ta umarce shi ya tura rubutaccen bayani zuwa shalƙwatar DSS a Abuja ko ta adireshin imel na hukumar cikin mako guda.

Hukumar ta kuma sanar da cewa ta tura kwafin wasiƙar zuwa ofishin jakadancin Amurka a Abuja, tana nuna cewa lamarin ya ja hankalin diflomasiyyar ƙasashen waje duba da matsayin Sowore na zama a Nijeriya da Amurka. Ta gargaɗe shi da cewa a matsayinsa na wanda ke neman muƙamin siyasa, dole ya nuna ƙwarewa da ladabi a magana da aiki, saboda hakan na da muhimmanci wajen inganta zaman lafiya da tsaro a ƙasar.

DSS ta nanata cewa aikinta na doka shi ne tabbatar da cewa ’yan Nijeriya ba sa samun labaran yaudara ta hanyar yaɗa ƙarya ko farfaganda, tana mai cewa idan Sowore bai janye maganarsa ba cikin wa’adin da aka bayar, to za ta ɗauki matakan da ta dace bisa doka.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
Next Post
Xi Ya Halarci Taron Kungiyar BRICS Ta Yanar Gizo

Xi Ya Halarci Taron Kungiyar BRICS Ta Yanar Gizo

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version