Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home KASASHEN WAJE

Dubban Mutane Sun Yi Zanga-Zanga A Kasar Togo

by Tayo Adelaja
September 11, 2017
in KASASHEN WAJE
1 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Dubban mutane sun yi zanga zanga a duk fadin kasar Togo a ranar Larabar makon da ya gabata, suna bukatar kawo karshen mulkin shekara da shekaru da shugaban kasar Faure Gnassingbe da iyalinsa suke yiwa kasar.

Shugabanin jam’iyyun masu hamayya na kasar ne suka bukaci dubban mutane da su fatsama titunan Lome babban birnin kasar da wasu biranen kasar, su bukaci shugaba Gnassinge ya sauka daga kan ragamar mulki, bayan wa’adinsa ya kare a shekara ta 2020,  idan Allah ya kaimu. Haka kuma sun bukaci a yiwa tsarin mulkin kasar kwaskwarima domin kayyade wa’adin mulkin shugaba.

A shekarar 1992 aka zartar da wata doka da ta yi tanadin wa’adi biyu wa shugaban kasa, to amma mahaifin shugaba Gnassingbe, marigayi Gnassingbe Eyadema ya soke wannan doka bayan shekaru goma.

Zanga zanga makamancin wannan da aka yi a watan Augusta ta buge da zama tarzoma har ma jami’an tsaro suka kashe mutane biyu

A shekara ta 2005 shugaba Faure Gnassingbe ya dare kan ragamar mulki bayan rasuwar mahaifinsa wanda ya share shekaru talatin da takwas yana jan ragamar mulkin basar Togo. A ranar Talatar makon da ya gabata ne dai Majalisar Ministocin kasar tayi na’am da wata shawarar da aka gabatar na mayar da kayyade wa’adin mulkin shugaban kasa.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Nahiyar Afrika: An Kama Boka Akan Satar Mota A Kenya

Next Post

Zaben 2019: Gwamnoni Da Ministoci Na Goyon Bayan Buhari Ya Zarce —Gwamna El-rufai

RelatedPosts

Mijin Sarauniya Elizabeth Ta Ingila Ya Mutu

Mijin Sarauniya Elizabeth Ta Ingila Ya Mutu

by Muhammad
1 week ago
0

Rahotanni daga Fadar Buckingham ta kasar Ingila sun tabbatar da...

Nijer

Matan Nijer Sun Dage Kan ‘Yancinsu Bayan Kotu Ta Sako Wasu Shugabanninsu

by Muhammad
4 weeks ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Hukumomi a jamhuriyar Nijer sun sako...

Magufuli

Muhimman Abubuwa Goma Game Da Tsohon Shugaban Tanzaniya John Magufuli

by Muhammad
4 weeks ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Al'ummar kasar Tanzania suna zaman makokin...

Next Post

Zaben 2019: Gwamnoni Da Ministoci Na Goyon Bayan Buhari Ya Zarce —Gwamna El-rufai

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version