Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Duk Da Matsalar Tsaro, Nijeriya Na A Hannu Na Gari – Lai Mohammed

by
12 months ago
in RAHOTANNI
1 min read
Raba Kasa
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Daga Mahdi M. Muhammad,

Ministan Yada labarai da al’adu, Alhaji Lai Mohammed ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa, “duk da matsalolin tsaro da muke fuskanta a yanzu, Nijeriya na cikin amintattun hannaye’’.

Ministan ya bayar da tabbacin ne ranar Alhamis a Abuja lokacin da basaraken gargajiyar na Iyin-Ekiti, Oba Adeola Ajakaiye, Oluyin na Iyin-Ekiti suka kai masa ziyarar ban girma.

Labarai Masu Nasaba

2023: Kotu Ta Yi Fatali Da Karar Emefiele Kan Ministan Shari’a Da INEC

Hukumar Alhazan Kogi Ta Fara Shirin Bita Ga Maniyyata

Ya kara da cewa, “bai kamata mu rinka yin wani abu da bai kamata ba ga kasar don hasashen ranar gobe kiyama. Yana da muhimmanci ga shugabanninmu a kowane mataki su bai wa mutane sakon bege a maimakon yin tsokaci da zai iya kara rura wutar rikici.”

Lai Mohammed ya yi kira musamman ga sarakunan gargajiya a kasar nan da su hada kai da gwamnatocin jihohinsu don tabbatar da zaman lafiya da tsaro.

“Sarakunan gargajiya na da matukar muhimmanci wajen wanzar da zaman lafiya da tsaro a yankin su. Wannan shine dalilin da ya sa ba za su iya ba kuma ba za a yi watsi da su ba, yayin da muke neman dawo da zaman lafiya da tsaro a duk fadin kasar,” in ji shi.

Ministan ya fada wa basaraken, wanda ya zo neman hadin gwiwa kan bunkasa yawon bude ido a yankinsa, cewa ba za a samu nasarar yawon shaklkatawa ba tare da tsaro ba.

Ya yi alkawarin sanya Kogon Esa da Okuta Abanijorin, wuraren shakatawa na bai daya na Iyin-Ekiti, a kan taswirar kasa da ta duniya don jan hankalin masu yawon bude ido.

ADVERTISEMENT

A nasa bangaren, Oba Ajakaiye ya tabbatar wa da Ministan sha’awarsa da jajircewarsa don zaman lafiya a kasar.

Ya kuma jaddada cewa yin amfani da wuraren yawon bude ido a yankinsa zai bunkasa tattalin arzikin garin, jihar Ekiti da klkasa baki daya.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Za A Tantance Al’umma Masu Karamin Karfi A Jihar Katsina

Next Post

Cutar Sikila Ga Dalibai: Hanyoyin Da Ya Kamata Makarantu Su Bi Don Taimakawa

Labarai Masu Nasaba

2023: Kotu Ta Yi Fatali Da Karar Emefiele Kan Ministan Shari’a Da INEC

2023: Kotu Ta Yi Fatali Da Karar Emefiele Kan Ministan Shari’a Da INEC

by Khalid Idris Doya
2 days ago
0

...

Hukumar Alhazan Kogi Ta Fara Shirin Bita Ga Maniyyata

Hukumar Alhazan Kogi Ta Fara Shirin Bita Ga Maniyyata

by Ahmed Muhammad Dan'asabe
6 days ago
0

...

Fashewar Gas: An Zakulo Gawarwaki 9 A Ginin Da Ya Rushe A Kano

Fashewar Gas A Kano: Ministar Jinkai Ta Nemi A Dauki Matakan Riga-kafi

by
6 days ago
0

...

Baki Biyu Bai Dace Da Matsayin Amurka Ba

Baki Biyu Bai Dace Da Matsayin Amurka Ba

by CMG Hausa
6 days ago
0

...

Next Post
Cutar Sikila Ga Dalibai: Hanyoyin Da Ya Kamata Makarantu Su Bi Don Taimakawa

Cutar Sikila Ga Dalibai: Hanyoyin Da Ya Kamata Makarantu Su Bi Don Taimakawa

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: