Yusuf Shuaibu">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home TATTALIN ARZIKI

Duk Da Matsin Tattalin Arziki Tsadar Kaya Ya Tashi Zuwa Kashi 14.89

by Yusuf Shuaibu
December 17, 2020
in TATTALIN ARZIKI
2 min read
Matsin Tattalin Arziki
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

 Hauhawar farashin kayayyaki ya karu zuwa kashi 14.89 a cikin watan Nuwambar shekarar 2020, fiye da na kashi 14.23 wanda aka samu a watan Oktobar shekarar 2020. Masana sun bayyana cewa, wannan karuwear hauhawar farashin da ake samu ya samo asali ne sakamakon rufe iyakokin kasar nan. Rahoton farashin kayayyaki wanda hukumar kididdiga ta kasa (NBS) a ranar Talata, ya nuna cewa kayayyakin abinci ya karu da kashi 18.30 a cikin watan Nuwambar shekarar 2020, idan aka kwatantashi da na kashi 17.38 wanda aka samu  a watan Oktoban shekarar 2020.

“Farashin kayayyakin da suka karu sun hada da biredi da hatsi da taankali da doya da alkama da kifi da kayayyaki itatuwa da kayayyakin lambu da man girke-girke.”

samndaads

A hannu daya kuma, dukkan wani kayayyaki wanda ba na noma ba ya ragu da kashi 11.05 a watan Nuwambar shekarar 2020, idan aka kwatanta da na kashi 11.14 wanda aka samu a watan Oktobar shekarar 2020.

Wasu masana masu suna Mosope Arubayi da Ibukun Omoyeni a nasu ra’ayin suna ganin cewa, an fara samun hauhawar farashin kayayyaki ne tun a shekarar 2016, wanda a duk watan 12 sai an samu karin da ba a taba samu ba.

Sun kara da cewa, idan ba a daauki matakan da suka dace ba kafin karshen wannan shekara, to haka za a ci gaba da fuskantar hauhawar farashin kayayyaki a cikin kasar nan.

A kwanakin nan ne, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayyana yuwuwar bude iyakokin kasar nan.

Masana sun ci gaba da cewa, idan aka samu jinkirin samar da kayayyakin abinci a shekarar 2021, to ba za a samu wani canji a kan yadda ake gani ba a wannan  shekara, yana da matukar mahimmanci a bude iyakokin kasar nan kafin shekarar nan ta kare.

SendShareTweetShare
Previous Post

Rashin Tsaro: Akasarin Jihohin Arewa Maso Yamma Sun Rufe Makarantu

Next Post

Gina Bututun Gas: China Ta Amince Da Bai Wa Nijeriya Bashin Dala Biliyan 2.6

RelatedPosts

Kasafin 2021

Buhari Zai Kaddamar Da Cibiyar Mai Da Gas Ta Kasa A Legas

by Yusuf Shuaibu
12 hours ago
0

Shugaban kasa Muhammadu Buhari zai kaddamar da cibiyar mai da...

An Nemi Matakan Gwamnati Su Rage Yawan Mukaman Siyasa Don Zuba Jari A Noma

Bai Kamata A Fake Da Tallafi A Azabtar Da ’Yan Nijeriya Ba, Inji NLC

by Yusuf Shuaibu
12 hours ago
0

kungiyar kwadagon Nijeriya (NLC) ta bayyana cewa, bai kamata gwamnatin...

Kasafin 2021: Buhari Da Osinbajo Za Su Ci Abinci Da Balaguron Naira Biliyan N3.4

Kasafin 2021: Buhari Da Osinbajo Za Su Ci Abinci Da Balaguron Naira Biliyan N3.4

by Yusuf Shuaibu
12 hours ago
0

Shugaban kasa Muhammadu Buhari da mataimakinsa Yemi Osinbajo za su...

Next Post
Gina Bututun Gas

Gina Bututun Gas: China Ta Amince Da Bai Wa Nijeriya Bashin Dala Biliyan 2.6

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version