Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Duk Da Za Mu Sayi Manyan ‘Yan Wasa, Ba Zan Saki Matasanmu Ba – Lampard

by
2 years ago
in WASANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Kociyan kungiyar kwallon kafa ta Chelsea, Frank Lmapard, ya bayyana cewa zai cigaba da amfani da matasan ‘yan wasa a kungiyar tasa duk da cewa yanzu zasu sayi ‘yan wasa a kasuwar saye da sayar da ‘yan wasa ta watan Janairu.

Lampard ya bayyana hakane bayan da aka tashi daga wasan da Chelsea ta tsallake rijiya da baya, ta kai matakin gaba na kungiyoyi 16 a gasar Zakarun Turai, bayan da ta tsira a hannun Lille da ci 2-1, a gidanta na Stamford Bridge.

Kungiyar ta mamaye wasan a kusan gaba dayan lokacin, inda ta samu nasarar da take matukar bukata daga kwallayen da Tammy Abraham and Cesar Azpilicueta suka ci mata a kashin farko na wasan.

Labarai Masu Nasaba

Wasan Damben Cin Mota: An Fara Fafatawa A Kano

Har Yanzu Ban Hakura Da Lashe Firimiya Ba, Cewar Klopp

Abraham mai shekara 22, shi ne ya fara zura kwallo a raga da kwallonsa ta 13 a kakar bana bayan minti 19 da shiga fili, bayan da Willian ya cilla masa wata kwallo kuma wannan kwallo da Abraham ya ci ta sa ya zama dan wasan Ingila na farko da ya taba ci wa Chelsea kwallo 13 a gasa a kaka daya kacal, tun bayan Lampard da ya ci mata 17 a kakar wasa ta 2012-13 kuma Abraham din yana da damar wuce Lampard a wannan bajinta, kasancewar a yanzu ko rabin kakar ba a yi ba.

“Zan cigaba da amfani da matasan ‘yan wasan da nake dasu saboda dasu muka fara hakan yana nufin bazan iya daina amfani dasu ba saboda nan gaba sune zasu kasance jagororin wannan kungiyar tamu” in ji Lampard

Bayan kammala wasan rukunin nasu na 8, (Group H), Balencia wadda ta bi Ajad har gida ta doke ta 1-0, tana da maki 11 da yawan kwallo 2, Chelsea na bi mata baya ita ma da maki 11 da yawan kwallo 2.

Ajad, wadda ta ga samu ta ga rashi ta yi waje a matsayi na uku da maki 10 da yawan kwallo shida, yayin da Lille ta kasance ta karshe da maki daya da bashin kwallo 10 kuma za a fitar da jadawalin wasannin mataki na gaba na gasar ta Zakarun Turai, a ranar Litinin, a birnin Nyon, na Switzerland da karfe 12:00 na rana agogon Nijeriya.

Tarihin da aka kafa a wasan Chelsea Da Lille

Da wannan nasara da Chelsea ta samu, Lampard ya zama kociya dan Ingila na farko da ya kai wata kungiya matakin gaba na sili-daya-kwale na gasar ta Zakarun Turai, bayan da ya karbi jan ragamar dukkanin wasanni shida na rukuni na kungiyar, tun bayan da Harry Redknapp ya yi wannan bajinta da Tottenham a kakar wasa ta shekara ta  2010 zuwa 2011.

Maki daya kawai Lille ta samu a wannan kaka da ta zamar mata mafi muni a matakin rukuni na gasar ta cin Kofin Zakarun Turai na Champions League sannan kungiyar ta Lille ta yi wasa shida a gidan kungiyoyin Ingila a manyan gasar Turai kuma ba ta taba yin nasara a ko da daya ba.

Loic Remy ya zama dan wasa na bakwai da ya ci wa Chelsea kwallo kuma ya ci kungiyar a filinta na Stamford Bridge a gasar ta Zakarun Turai ta Champions League, bayan Samuel Eto’o da Fernando Torres da Diego Costa da Michael Ballack da Dabid Luiz da kuma Willian.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Inason Kafa Irin Tarihin Messi —Ansu Fati

Next Post

Zuwan Musulunci Da Sauye-Sauye Da Ya Kawo A Cikin Rayuwar Hausawa Ta Fannin Addini Da Al’ada

Labarai Masu Nasaba

dambe

Wasan Damben Cin Mota: An Fara Fafatawa A Kano

by Abba Ibrahim Wada
4 days ago
0

...

klopp

Har Yanzu Ban Hakura Da Lashe Firimiya Ba, Cewar Klopp

by Abba Ibrahim Wada
4 days ago
0

...

barcelona

Barcelona Ta Sa Hukumar La Liga Asarar Makudan Kudade

by Abba Ibrahim Wada
4 days ago
0

...

Nijeriya Ta Dakatar Da Shiga Wasannin Kwallon Kwando Tsawon Shekara Biyu

Nijeriya Ta Dakatar Da Shiga Wasannin Kwallon Kwando Tsawon Shekara Biyu

by Abba Ibrahim Wada
4 days ago
0

...

Next Post
Zuwan Musulunci Da Sauye-Sauye Da Ya Kawo A Cikin Rayuwar Hausawa Ta Fannin Addini Da Al’ada

Zuwan Musulunci Da Sauye-Sauye Da Ya Kawo A Cikin Rayuwar Hausawa Ta Fannin Addini Da Al’ada

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: