Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Duk Mai Neman Maganin Talauci Ya Rungumi Kasuwanci – Alhaji Mai Dubji

by
12 months ago
in LABARAI
1 min read
Duk Mai Neman Maganin Talauci Ya Rungumi Kasuwanci – Alhaji Mai Dubji
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, Kano

Daya daga cikin dattawan Kasuwar Kantin Kwari Alhaji Muhammad Abdullahi Mai Dubji ya bayyana cewa duk mutumin da yake so ya samu maganin talauci a rayuwarsa, ya rungumi kasuwanci.

Ya bayyana haka ne a zantawarsa da wakilinmu a Kano.
Da yake tsokaci a kan muhimmanci bunkasa kasuwanci, ya bayyana cewa yanzu dai ko hasidin iza hasada ya gamsu tare da amincewa gine-ginen shaguna da wuraren gudanar da harkokin kasuwanci da Gwamnan Jihar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje ke ta shimfida wa Kanawa ya zama alhairin da za a jima ana tuna shi dasu.

Labarai Masu Nasaba

Masarautar Zazzau Ta Mayar Da Martani Kan Zargin Jama’atu Na Kai Karar Sarkinta

Kamfanin Simintin Dangote Ya Samu Ribar Biliyan 410 A Wata Uku

Mai Dubji ya yaba da manyan gine-ginen shaguna da wuraren kasuwanci da ahalin yanzu dubun dubatar matasa ke samun hanyoyin dogaro da kai tare da samun abin sawa abakin salati.
Alhaji Mai Dubji ya ci gaba da cewa wadannan gine-gine da Khadimul Islam ke kwararawa a Kano ya taimaka kwarai da gaske wajen jawo masu sha’awar zuba jari a harkokin kasuwanci ci gaba kwararowa Jihar Kano.

Yace mayan da tsoffin gidajen tsohuwar kasuwar kantin kwari zuwa sabbi irin na zamani, ya baiwa matasa maza da mata samun ayyukanyi, kuma kamar yadda aka sani wadannan gidajen duk mallakar Jama’a ne, yanzu kamfanoni suka sabunta gininsu tare da sayarwa masu bukata.

Kamar yadda aka sani, babban burin Gwamnatin Jihar Kano shi ne bunkasa Kasuwanci sannan da kyakkyawan fatan da Gwamna Ganduje yake dashi na ganin ‘yan kasuwa sun mallaki wadannan wuraren a Jihar Kano.

A karshe Alhaji Muhammad Abdullahi Mai Dubji ya jinjinawa kokarin Gwamnatin Jihar Kano karkashin jagorancin Gwamna Ganduje bisa kyakkyawar manufarta na Inganta harkokin kasuwanc, Wanda haka ke kara tabbatarwa da Jihar matsayinta na cibiyar ciniki a fadin afrika.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Gwamna Bagudu Ya Bukaci karin Zuba Jari A Sana’ar Kiwon Kifi

Next Post

Zhao Xinzhu: Basiniya ‘Yar Kasuwa Da Ta Yi Kokarin Samun Tambari Da Suna Ta Hanyar Kirkire-kirkire, Kulawa Da Kuma Kauna

Labarai Masu Nasaba

Masarautar Zazzau Ta Mayar Da Martani Kan Zargin Jama’atu Na Kai Karar Sarkinta

Masarautar Zazzau Ta Mayar Da Martani Kan Zargin Jama’atu Na Kai Karar Sarkinta

by Abubakar Abba
3 hours ago
0

...

Kamfanin Simintin Dangote Ya Samu Ribar Biliyan 410 A Wata Uku

Kamfanin Simintin Dangote Ya Samu Ribar Biliyan 410 A Wata Uku

by
8 hours ago
0

...

Mutum 5 Sun Mutu Kan Rikicin ‘Yan Kasuwa Da ‘Yan Babura A Abuja

Mutum 5 Sun Mutu Kan Rikicin ‘Yan Kasuwa Da ‘Yan Babura A Abuja

by
9 hours ago
0

...

Ministar Kudi Ta Dakatar Da AKanta Janar Na Kasa Kan Zargin Badakalar Biliyan 80

Ministar Kudi Ta Dakatar Da AKanta Janar Na Kasa Kan Zargin Badakalar Biliyan 80

by
10 hours ago
0

...

Next Post
Zhao Xinzhu: Basiniya ‘Yar Kasuwa Da Ta Yi Kokarin Samun Tambari Da Suna Ta Hanyar Kirkire-kirkire, Kulawa Da Kuma Kauna

Zhao Xinzhu: Basiniya 'Yar Kasuwa Da Ta Yi Kokarin Samun Tambari Da Suna Ta Hanyar Kirkire-kirkire, Kulawa Da Kuma Kauna

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: