Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home WASANNI

Duniya Za Ta Sha Mamaki Idan Muka Je Gidan PSG A Faransa -Koeman

by Muhammad
February 19, 2021
in WASANNI
2 min read
Koeman
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Kocin kungiyar kwallon kafa ta Barcelona Ronald Koeman, ya ce ba shakkah kungiyar kwallon kafa ta Paris Saint German ta yi musu wanka da ruwan sanyin da ke bayyana gaskiyar halin da suke ciki na matsalolin da suka tilasta musu fuskantar kalubale.

Koeman ya bayyana haka ne yayin da yake tsokaci kan lallasa su da PSG ta yi da ci 4-1 a haduwarsu ta farko a zagayen gasar Zakarun Turai na biyu da aka fafata a filin wasa na Nou Camp dake birnin Barcelona a kasar Spaniya.

samndaads

Koeman ya bayyana cewa duk da cewa an zura musu kwallaye hudu a raga amma duk da haka ba su fitar da ran cewa za su samu nasara ba a kan kungiyar ta PSG idan an buga wasa na biyu a kasar Faransa.

“Duk da haka ina da kwarin gwiwar cewa zamu samu nasara a kansu a fafatawa ta gaba da zamuyi dasu saboda kwallo ce komai zai iya faruwa idan munje kasar Faransa buga wasa na biyu kuma ina fatan zamu samu nasara” in ji Koeman

Yayin wasan na ranar Talata dai matashin dan wasan PSG Kylian Mbappe ya nuna kansa inda ya ci kwallaye uku, ya yin da shima dan wasa Moise Kean ya ci kwallo daya, a bangaren Barcelona kuwa Messi ne ya ci mata kwallon guda daga bugun fanareti.

Sai dai kaftin din Barcelona Lionel Messi yana shan caccaka daga wasu magoya bayan kungiyar, da kuma masu sharhi kan kwallon kafa, dangane da gazawar da wasu ke ganin yayi wajen taimakawa Barcelona ya yin wasan da PSG ta lallasa su da 4-1 har gida Camp Nou a gasar Zakarun Turai.

Tsohon dan wasan Chelsea Joe Cole ne na baya bayan nan da ya caccaki Messi, wanda ya ce alamu sun nuna cewa zuciyar kaftin din ba ta tare da kungiyar sa saboda gaba daya bai buga abinda akayi zaton zai buga ba.

Joe Cole ya kuma gargadi kociyan Manchester City Pep Guardiola da cewar, ya guji kulla yarjejeniya da Messi domin a cewarsa a halin yanzu kallon kitse ake yiwa rogo domin ba irin Messin da aka sani bane a shekarun baya.

A kakar wasan da ta gabata dangantaka tayi tsami tsakanin Messi da Barcelona, bayan da suka sha mummunan kayi a wasan gasar Zakarun Turan da Bayern Munich ta lallasa su da ci 8-2 a zagayen kusa dana kusa dana karshe.

A waccan lokacin dai Messi yayi yunkurin tilastawa Barcelona kyale shi ya sauya sheka kamar yadda yake kunshe cikin yarjejeniyar sa da kungiyar, wadda a karkashinta yake da zabin rabuwa da ita a karshen kakar wasa, ko da kuwa wa’adin yarjejeniyar bai kare ba.

A halin yanzu kungiyoyin da ake alakanta Messi da su sun hada da kungiyar kwallon kafa ta PSG wadda ake ganin zaije ya hadu da tsohon abokinsa Neymar da kuma Manchester City wadda zai hadu da tsohon mai koyar dashi wato Pep Guardiola wadda kuma a shekarar bara suka soma tuntubar juna.

SendShareTweetShare
Previous Post

Shirin Gasar Kofin Afirka: Babu Tabbas Ko Nijeriya Za Ta Gayyaci Ahmed Musa

Next Post

Sai A Watan Gobe Pogba Zai Dawo Daga Jinya -Solkljaer

RelatedPosts

Ko Kun San Rayuwar Tiger Woods A Wasan Golf?

Ko Kun San Rayuwar Tiger Woods A Wasan Golf?

by Sulaiman Ibrahim
2 days ago
0

Daga Abba Ibrahim Wada Dan wasa Tiger Woods dai na...

Ban Yi Da-na-sanin Barin Barcelona Ba – Suares

Ban Yi Da-na-sanin Barin Barcelona Ba – Suares

by Sulaiman Ibrahim
2 days ago
0

Daga Abba Ibrahim Wada Tsohon dan wasan gaba na kungiyar...

Man City Ta Kama Hanyar Wasan Kusa Da Karshe A Kofin Zakarun Turai

Man City Ta Kama Hanyar Wasan Kusa Da Karshe A Kofin Zakarun Turai

by Sulaiman Ibrahim
2 days ago
0

Daga Abba Ibrahim Wada Dan wasan tsakiyar kungiyar kwallon kafa...

Next Post
Pogba

Sai A Watan Gobe Pogba Zai Dawo Daga Jinya -Solkljaer

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version