Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

el-Rufai: Cikin ‘Yan Majalisar Dokokin Kaduna Ya Duri Ruwa

by
2 years ago
in RAHOTANNI
2 min read
el-Rufai: Cikin ‘Yan Majalisar Dokokin Kaduna Ya Duri Ruwa
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Rahotanni sun kawo cewa ‘yan majalisar dokokin Jihar Kaduna sun shiga alhini da rudani sakamakon sanarwar da Gwamnan Jihar kaduna, Malam Nasir El-Rufai ya yi a ranar Asabar, na cewar sakamakon gwaji ya nuna yana dauke da cutar Coronabirus.

Wakilinmu ya ruwaito cewa, sanarwar da El-Rufai ya yi ya sanya fargaba a zukatan wasu ‘yan majalisa musamman wadanda suka yi aiki dab da dab da shi a makon da ya gabata, domin basu san ya yi gwajin ba.

Wakilinmu ya ruwaito cewa, wasu mambobin majalisar ma sun shiga killace kansu tun bayar sanarwar, yayin da Shugaban ma’aikatan Gwamnan, Mohammed Sani Dattijo wanda kan kasance tare dashi a koda yaushe ya yi gwaji kuma sakamako gwajin ya nuna cewa baya dauke da cutar.

Labarai Masu Nasaba

Hukumar Alhazan Kogi Ta Fara Shirin Bita Ga Maniyyata

Fashewar Gas A Kano: Ministar Jinkai Ta Nemi A Dauki Matakan Riga-kafi

A wata sanarwa da Uwargidan Gwamnan Jihar kaduna, Hajiya Hadiza El-Rufai, ta wallafa a shafin ta na Twitter, ta bayyana cewa za a kai samfarin jininta gwaji a ranar Lahadi sannan ta yi godiya ga ‘yan Najeriya kan addu’o’insu da fatan alkhairi da suka yiwa Mijin na ta, wato Gwamnan Malam Nasir El-rufai.

Akwai rahotannin dake bayyana cewa, tuni suma Mataimakiyar Gwamnan Jihar, Dakta Hadiza Balarabe da Sakataren Gwamnatin jihar, Malam Balarabe Lawal Abbas, suma sun yi nasu gwajin.

Sai dai wakilinmu ya  tattaro cewa tun bayan sanarwar wasu kwamishinoni da hadiman gwamanan  sun shiga damuwa, a inda daya daga cikin kwamishinan ya bayyana cewa koda dai bai hadu da gwamnan ba na tsawon makonni biyu da suka gabata, amma ya hadu da manyan jami’an gwamnati wadanda suka hadu da gwamnan.r

Wakilinmu ya ruwaito cewa koda dai gwamnan bai yi tafiya zuwa wajen kasar ba a wata guda da ya gabata, kuma bai halarci taron gwamnonin APC da shugaban kasa Buhari ba a ranar 16 ga watan Maris, amma ya kasance a taron majalisar tattalin arziki a Abuja a ranar 19 ya watan Maris inda ya hadu da wasu daga cikin takwarorinsa Gwamnoni ciki har da Bala Mohammed na Jihar Bauchi wanda shi ma ya tabbatar ya na dauke da da cutar ta korona barus.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

’Yan Sanda Sun Damke ‘Yan Fashi Biyar

Next Post

COVID-19: Jamus Za Ta Kwashe ’Yan Kasarta Daga Nijeriya

Labarai Masu Nasaba

Hukumar Alhazan Kogi Ta Fara Shirin Bita Ga Maniyyata

Hukumar Alhazan Kogi Ta Fara Shirin Bita Ga Maniyyata

by Ahmed Muhammad Dan'asabe
3 days ago
0

...

Fashewar Gas: An Zakulo Gawarwaki 9 A Ginin Da Ya Rushe A Kano

Fashewar Gas A Kano: Ministar Jinkai Ta Nemi A Dauki Matakan Riga-kafi

by
3 days ago
0

...

Baki Biyu Bai Dace Da Matsayin Amurka Ba

Baki Biyu Bai Dace Da Matsayin Amurka Ba

by CMG Hausa
3 days ago
0

...

Fashewar Gas: An Zakulo Gawarwaki 9 A Ginin Da Ya Rushe A Kano

Fashewar Gas: An Zakulo Gawarwaki 9 A Ginin Da Ya Rushe A Kano

by
5 days ago
0

...

Next Post

COVID-19: Jamus Za Ta Kwashe ’Yan Kasarta Daga Nijeriya

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: