Khalid Idris Doya">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

El-Zakzaky Ya Raba Wa ‘Yan Gudun Hijira Kyautar Magunguna Da Barguna A Katsina

by Khalid Idris Doya
January 3, 2021
in LABARAI
2 min read
El-Zakzaky
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Shugaban ‘yan uwa Musulmai da aka fi saninsu da (Shi’a) Shaikh Ibraheem El-Zakzaky, a karo na biyu ya sake kai tallafi wa ‘yan gudun hijira da ke zaune a karamar hukumar Faskari ta cikin jihar Katsina a makon da ta gabata.

Malam Rabiu Abdullahi Funtuwa shi ne ya wakilci El-Zakzaky yayin mika tallafin, ya shaida cewar, “Wannan sako ne daga shugabanmu Shaikh Ibraheem Zakzaky, da ya bayar domin a kawo muku wannan tallafin da suka kunshi kayayyakin sanyi, Barguna guda 300, gidajen Sauro guda 300 da kuma magunguna daban-daban domin jinyar rashin lafiya idan bukatar hakan ta taso.”

samndaads

“Shugaban namu ya saba irin wannan aikin, idan za ku tuna a karin farko ya kawo muku tallafin abinci, amma yanzu bisa nazarin yanayin sanyi ya sanya kawo muku kayayyakin da za su fi taimakonku a irin wannan lokacin na sanyi da ake ciki sakamakon rabaku da gidajenku ba don ku na so ba; wannan tallafin ya zo ne bisa damuwa da halin da kuke shi da shi Malamin namu yi,” inji shi.

El-Zakzaky ya bayyana matsalolin tsaron da har suke haifar da ‘yan gudun hijira tabbas gazawar gwamnatoci ne wanda hakan na samu asali daga zalumcin da ake yi wa al’umma.

Daya daga cikin wadanda suka amfana da tallafin, Malama Bilkisu Garba ta bayyana godiyarta ga Malamin a bisa tallafin da ya ba su, tana mai cewa damuwa da halin da suke ciki ma kawai da ya yi abun yabo ne, ta masa fatan kaifi.

Tunin kuma aka rabar da barguna da magunan ga wadanda aka bada tallafin dominsu kai tsaye inda suka nuna matukar farin cikinsu a bisa wannan tallafin da suka samu.

SendShareTweetShare
Previous Post

Yakamata A Wayar Da Kan Al’ummar Muhimmancin Karbar Katin Zama Dankasa

Next Post

An Bude Cibiyar Koyar Da Aikin Gona Mai Zaman Kanta A Kano

RelatedPosts

Za A Kulle Duk Layin Da Ba A Yi Rijistarsa Da Katin Dan Kasa Ba Ranar 9 Ga Fabrairu

Za A Kulle Duk Layin Da Ba A Yi Rijistarsa Da Katin Dan Kasa Ba Ranar 9 Ga Fabrairu

by Khalid Idris Doya
4 hours ago
0

Gwamnatin Tarayya ta kara wa’adin da aka diba wa ’yan...

Sayar Da Kadarorin Gwamnati Zai Taimaki ‘Yan Nijeriya, Inji Minista

Sayar Da Kadarorin Gwamnati Zai Taimaki ‘Yan Nijeriya, Inji Minista

by Khalid Idris Doya
4 hours ago
0

Ministar Kudi, Zainab Ahmed, ayau Juma’a, ta ce shirin Gwamnatin...

Zakzaky

Matar Sheikh EL-Zakzaky Ta Kamu Da Korona, In Ji Danta

by Khalid Idris Doya
9 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Matar Shugaban Kungiyar Musulunci a Nijeriya...

Next Post
Aikin Gona

An Bude Cibiyar Koyar Da Aikin Gona Mai Zaman Kanta A Kano

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version