Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

#EndSARS: Kwamitin Bincike Ya Biya Mai Shigar Da Korafi Diyyar N150,000

by Muhammad
November 28, 2020
in LABARAI
1 min read
Diyyar
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Khalid Idris Doya

Kwamitin binciken cin zarafin bil adama da gwamnatin jihar Ekiti ta kafa domin binciko zarge-zargen cin zarafin da jama’an rushashshiyar tawagar SARS suka aikata, kwamitin ya amince da bada shawarar biyan diyyar naira 150,000 ga wani da rikicin EndSARS ya shafa wato Mista Adaramola Olusola.

samndaads

Shugaban kwamitin, Justice Cornelius Akintayo (mai ritaya) shi ne ya bada wannan shawarar biyan diyyar a jiya yayin da ke nazartar barnar da aka yi ga motar wani mai shigar da korafi yayin zanga-zangar EndSARS.

Justice Akintayo ya lura kan cewa Mista Olusola ya gabatar da kwararan shaidu a gaban kwamitin inda ya yi zargin cewa an lalata masa motarsa kirar Peagout 505 saloon mai lamba Reg. No YEE 310 AA a yayin zanga-zangar EndSARS ta ranar 19 ga watan Oktoban 2020 da karfe 5:30 da 7:00 na yammaci a daidai layin Dalimore Junction, Ado Ekiti a inda ya ajiye motarsa domin gudanar da harkokin gabansa.

Shugaban kwamitin ya kara da cewa mambobin kwamitin sun je domin ganin irin barnar da aka masa wanda wasu ‘yan daba suka aikata, inda aka farfasa masa gilan motar da wasu ababen jikinta.

“Don haka mun baiwa gwamnatin jihar shawara ta biya diyyar lalata motar da aka yi masa domin ya samu damar gyarawa. Mun bada shawarar a biya shi naira dubu dari da amshin domin ya gyara barnar da aka masa bisa adalci.”

Kwamitin ya dage zaman nasa har zuwa ranar 1 ga watan Disamban 2020

SendShareTweetShare
Previous Post

Tsaron Kasa: Rundunar Sojin Sama Ta Jaddada Kudurinta Na Kare Nijeriya

Next Post

Kula Da Al’umma: NAF Ta Gudanar Da Binciken Cutar Daji A Osun

RelatedPosts

Man Fetur

Kudirin Dokar Man Fetur Zai Bai Wa Nijeriya Damar Cin Gajiyar Albarkatunsa – Majalisar Dattawa

by Muhammad
2 hours ago
0

Daga Muhammad Maitela, Shugaban majalisar dattawa, Sanata Ahmad Ibrahim Lawan...

Jobe

Ma’aikata Da ’Yan Fansho Ke Wawashe Rabin Kudin Katsina, Cewar Kwamishina Jobe

by Muhammad
2 hours ago
0

Daga Sagir Abubukar, Kwamishinan Kasafin Kudi da Tsare-tsaren Tattalin Arziki...

Rasuwar

Ana Cigaba Da Jimamin Rasuwar Mai Shari’ a Rabiu Danlami A Kano

by Muhammad
2 hours ago
0

Daga Haruna Akarada, Ana cigaba da gudanar da ta’aziyya ta...

Next Post
Cutar Daji

Kula Da Al’umma: NAF Ta Gudanar Da Binciken Cutar Daji A Osun

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version