Ibrahim Muhammad">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

‘’Fadada Kasuwanci Zai Taimakawa Samar Wa Matasa Aikin Yi’’

by Ibrahim Muhammad
January 17, 2021
in LABARAI
2 min read
Kasuwanci
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

An yi kira ga yan kasuwa akan idan suka sami dama su rika kokarin fadada harkokinsu domin zai bada damar cigaba da baiwa matasa damar koyon yin harkar kasuwanci dan dogaro dakai.

Shugaban sabon Katafaren Shagon saida kayayyakin amfanin gida na girke-girken mata mai suna “Bin Mustapha Plastic” dake kasuwar Wambai, Alhaji Abubakar Kabir Indabawa ya yi wannan kiran yayin bude shagon a ranar Laraba.

samndaads

Ya ce dama shagon na “Bin Mustapha Plastic and Kitchen” sun dade suna burin su samar dashi, sai yanzu Allah ya nufa aka bude don fara sana’ar kasuwanci musamman na kaya da suka danganci na bukatar Amare  da kawata gida a fannin girki.

Ya ce kara da cewa yawanci kayan da suka samar na  waje ne amma duk da haka suna da wani sashen da suke sai da wadanda ake a kasarnan kuma sun samar da shago ne don zamanantar da yanayin kasuwanci.

Ya ce harkar da suke gaba daya ta iyaye ce domin su za su aurar da ‘ya’ya mazaje kuma su suke sabunta dakunan iyalai kuma sabon wajen e da suka yi tanadii na saukakawa.

Ya kara da cewa suna da ma’aikata da suka kai guda 10 wanda suna da burin kara yawansu anan  gaba, don haka zai taimakawa samawa matasa aiki. Saboda haka masu hali su rika bude wani wajen kara bude wani wajen zai taimakawa al’umma ya kuma taimakawa kai da makota daka samu domin za su iya samun alkhairi saboda zuwan ka.

Alhaji Abubakar Kabir ya jaddada kira ga masu hali su rika bude masana’anta musamman a irin wannan yanayi da take ciki.Ya godewa dinbin al’umma da suka zo na nesa dana kusa don tayasu  murna aka zo aka bude waje lafiya. Cikin manyan yan kasuwa da suka albarkaci bude shagon na Bin Mustapha Plastic and Kitchen shugaban rukunin kantunan ELSAMAD da shima ya yi fatan alkhairi ga mamallakin sabon kantin.

Shima Tsohon kakakin hukumar yansanda na Kano Magaji Musa Majiya ya yi fatan albarka a jawabin da ya gabatar a wajen taron.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

An Jinjina Wa Ganduje Kan Matakan Yaki Da Shan Miyagun Kwayoyi A Tsakanin Zababbbun Shugabanni

Next Post

‘Yan Kasuwa Na Taimaka Wa Gwamnati Wajen Samar Da Aikin Yi Ga Al’umma, Cewar Ibrahim Abdullahi

RelatedPosts

Dan Majalisar Tarayya Ya Sabunta Katin Jam’iyyar APC A Funtuwa

Dan Majalisar Tarayya Ya Sabunta Katin Jam’iyyar APC A Funtuwa

by Ibrahim Muhammad
5 hours ago
0

Daga Hussaini Yero, Funtua  Dan majalisar Tarayya me wakiltar mazabar...

Sace Daliban Zamfara: Sarkin Musulmi Da Gwamna Tambuwal Sun Kai Ziyarar Jaje

Sace Daliban Zamfara: Sarkin Musulmi Da Gwamna Tambuwal Sun Kai Ziyarar Jaje

by Ibrahim Muhammad
5 hours ago
0

Daga Hussaini Yero, kasa da awa goma sha biyu da...

miyagun kwayoyi

Masu Garkuwa Da Mutane Muggan Kwayoyi Suke Bukata Matsayin Kudin Fansa – NDLEA

by Ibrahim Muhammad
7 hours ago
0

Daga Idris Aliyu Daudawa Shugaba kuma babban jami’i na Hukumar...

Next Post
Ibrahim Abdullahi

'Yan Kasuwa Na Taimaka Wa Gwamnati Wajen Samar Da Aikin Yi Ga Al’umma, Cewar Ibrahim Abdullahi

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version