Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home DAGA BIRNIN SIN

Farfesan Habasha: Salon Yaki Da Fatara Na Sin Abin Koyi Ne Ga Afrika

by Sulaiman Ibrahim
February 24, 2021
in DAGA BIRNIN SIN
1 min read
Farfesan Habasha: Salon Yaki Da Fatara Na Sin Abin Koyi Ne Ga Afrika
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga CRI Hausa

Wani kwararren kasar Habasha ya bayyana cewa, manyan nasarorin da kasar Sin ta samu a shirinta na yaki da talauci muhimmin darasi ne ga kasashen Afrika a kokarin da kasar ta yi wajen raya tattalin arzikinta da kuma tsame miliyoyin mutanenta daga kangin talauci.
A hirarsa da kamfaninn dillancin labarai na Xinhua, Costantinos Bt. Costantinos, farfesa a sashen nazarin dabarun shugabanci a jami’ar Addis Ababa ta kasar Habasha, ya ce, salon da kasar Sin ta yi amfani da shi ba kawai ya tsame mutane daga talauci ba ne, har ma ya taimaka wajen bunkasa karfin tattalin arzikin GDPn kasar, da cigabanta karkashin shirin na yaki da fatara.
Kwararren, wanda ya taba yin aiki a matsayin mashawarci a fannin raya tattalin arzikin kungiyar tarayyar Afrika, da hukumar raya tattalin arzikin Afrika ta MDD, ya kara da cewa, dandalin hadin gwiwar Sin da Afrika zai iya kasancewa a matsayin wani muhimmin dandalin da zai baiwa Sin da Afrika damar yin musayar kwarewa wajen yaki da fatara.
Game da yaki da fatarar, kwararren ya bayyana cewa kasar Sin tana da cikakkiyar kwarewa, kuma a shirye take ta yi hadin gwiwa da sauran kasashen duniya, wajen cimma wannan buri, inda ya jinjina manyan nasarorin da kasar Sin ta samu wajen tsame miliyoyin mutanenta daga talauci. (Ahmad)

SendShareTweetShare
Previous Post

An Kaddamar Da Rigakafin COVID-19 Na Kamfanin Sinopharm A Senegal, Masar Da Kawancen Larabawa

Next Post

Sin Tana Adawa Da Yadda Birtaniya Ta Yi Amfani Da Dandalin UNHRC Domin Shafa Mata Bakin Fenti

RelatedPosts

Ci Gaban Kasar Sin A Fannin Fasaha Ba Ya Tsoron Danniyar Amurka

Ci Gaban Kasar Sin A Fannin Fasaha Ba Ya Tsoron Danniyar Amurka

by Sulaiman Ibrahim
17 hours ago
0

Daga Bilkisu Xin A ranar 8 ga wata, ma’aikatar kasuwanci...

Takunkuman Amurka Da Birtaniya Kan Sin Sun Keta Dokokin Kasa Da Kasa

Takunkuman Amurka Da Birtaniya Kan Sin Sun Keta Dokokin Kasa Da Kasa

by Sulaiman Ibrahim
18 hours ago
0

Daga CRI Hausa Tsohon Jakadan Italiya a kasar Sin, Alberto...

Masanan Sin Da Afirka Suna Fatan Za A Kara Yin Mu’amalar Al’adu Da Juna

Masanan Sin Da Afirka Suna Fatan Za A Kara Yin Mu’amalar Al’adu Da Juna

by Sulaiman Ibrahim
18 hours ago
0

Daga CRI Hausa Kwalajin nazarin harkokin Afirka na kasar Sin,...

Next Post
Sin Tana Adawa Da Yadda Birtaniya Ta Yi Amfani Da Dandalin UNHRC Domin Shafa Mata Bakin Fenti

Sin Tana Adawa Da Yadda Birtaniya Ta Yi Amfani Da Dandalin UNHRC Domin Shafa Mata Bakin Fenti

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version