Fasahar Amfani Da ’Yan Sandan Mutum-Mutumi Ta Kasar Sin Na Iya Taimaka Wa Tsaro A Afirka
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fasahar Amfani Da ’Yan Sandan Mutum-Mutumi Ta Kasar Sin Na Iya Taimaka Wa Tsaro A Afirka

byCGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
Afirka

Ko makaho ya shafa, ya san yadda kimiyya da fasaha ke ci gaba taka gagarumar muhimmiyar rawa wajen kawo sauyi a daukacin sassan rayuwar bil’adama ta yau da kullum a duk fadin duniya. Kasar Sin na ci gaba da amfani da fasahohinta na zamanantarwa wajen kirkire-kirkire da kawo sabbin salo.

Da yake kasar tana shirin karbar bakuncin gasar wasannin motsa jiki ta duniya ta shekarar 2025 daga ranar 7 zuwa 17 ga Agusta, yanzu haka ta kera wasu mutum-mutumi na ’yan sanda da suka fara sintiri a hukumance a birnin Chengdu dake lardin Sichuan na yankin kudu maso yammacin kasar.

  • ‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
  • An Fara Binciken Mutuwar Wasu Ɗalibai 2 A Makarantar Kwana A Kano

’Yan sandan mutum-mutumin sun tsunduma aiki tare da jami’ai abokan aikinsu a dandalin Tianfu, daya daga cikin wuraren da aka fi samun kai-komon mutane da kafa a kalla 100,000 a kullum. Da kansu suke sauya wurin aiki a tsakaninsu duk bayan awa biyu zuwa uku inda suke nadar murya da bidiyon abubuwan dake faruwa tare da aikawa nan take ga jami’an ’yan sandan dake kusa. A ranar 16 ga Yunin da ya gabata ne aka fara gwada ayyukan ’yan sandan na mutum-mutumi da nufin kara inganta amfani da su a birane.

An saya musu fasahar iya sadarwa, da yadda za su iya ba da taimakon aikin ’yan sanda ga masu yawon bude ido, da kula da zirga-zirgar ababen hawa, sannan da kansu suke kai kansu wurin caji don tabbatar da cewa aikinsu bai tsaya ba. Akwai abubuwan mamaki da yawa da wadannan ’yan sanda ke iya yi ciki har da gano mara lafiya a cikin masu yawon bude ido tare da kiran tawagar kawo daukin gaggawa.

Wannan fasaha za ta iya taimakon kasashenmu na Afirka wajen shawo kan matsalolin tsaro da dama duba da cewa har yanzu muna da karancin jami’an tsaro. Kididdigar da na gani daga shafin rumbun bayanai na Wikipedia na nuna cewa, a Nijeriya, mai yawan al’umma fiye da miliyan 230, duk dan sanda daya yana ba da tsaro ne ga kusan mutane 1000 ko kuma a ce duk ’yan sanda biyu suna kula ne da tsaron mutum 2,000. Kazalika, idan aka leka sauran kasashenmu na Afirka ma za a ga irin wannan gibin.

Idan za a yi amfani da wannan fasaha ta ’yan sandan mutum-mutumin inji ana iya rage yawan jami’ai da ake jibgewa a wuraren shafaffu da mai tare da kai su yankunan da ake fama da matsalar tsaro musamman na karkara.

Kar wani ya yi tunanin ko idan an dauki ’yan sanda daga birane zuwa karkara kamar an yi musu ba daidai ba, a’a, a ko ina aiki ya kama dole a je. Kuma da kudin kasa ake biyansu albashi ba kudin ’yan birni ba kawai. Su ma mazauna birane za su ci gajiyar hakan, don ’yan sandan mutum-mutumin za su yi aiki babu kakkautawa, tun da ba su bukatar barci, ko cin abinci, ko zaga bayi, da sauran wasu abubuwa na lalurorin dan’adam. Tabbas, amfani da su, zai kara yalwata jami’an ’yan sanda da ake bukata wurin gudanar da ayyukan tsaro ta yadda za a share wa al’umma hawaye ta fuskar matsalar tsaron da ake fama da ita.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa
Daga Birnin Sin

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Next Post
PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde

PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version