Fashewar Tankar Mai: Minista Ya Jajanta Wa Al'ummar Neja Da Iyalan Mutum 59 Da Suka Mutu
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fashewar Tankar Mai: Minista Ya Jajanta Wa Al’ummar Neja Da Iyalan Mutum 59 Da Suka Mutu

bySulaiman
1 year ago
Yajin aiki

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, a ranar Litinin ya jajanta wa al’ummar Jihar Neja bisa rasuwar mutane 59 a wani haɗarin mota da ya ritsa da su a hanyar Bida-Agaie-Lapai ranar Lahadi.

 

A cikin saƙon ta’aziyya da mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Malam Rabi’u Ibrahim, ya sanya wa hannu, ya ce, lamarin ya girgiza Jihar Neja da ƙasa baki ɗaya.

  • Da Ɗumi-ɗumi: Tankar Mai Ta Fashe Ta Kashe Mutane 30 A Neja
  • Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Hada Hannu Da Kungiyar Kasashen Musulmi A Bangarori Daban-Daban

Ya yi addu’ar Allah ya ba iyalan mamatan ikon jure wannan babban rashin.

 

Idris ya ce: “Ina miƙa ta’aziyya ta ga gwamnati da al’ummar Jihar Neja da iyalai, abokai da ‘yan’uwan mutane 48 da suka rasa rayukan su a wani mummunan hatsari da ya auku a hanyar Bida-Agaie-Lapai a Jihar Neja da sanyin safiyar Lahadi, 8 ga Satumba, 2024.

 

“Wannan mummunan lamari ya girgiza ɗaukacin Jihar Neja da ma ƙasa baki ɗaya kuma ina yi wa duk waɗanda abin ya shafa a wannan lokaci mai zafi addu’a. Don haka ina taya al’ummar Jihar Neja da ma Nijeriya baki ɗaya alhinin wannan babban rashi.

 

“Allah ya jiƙan waɗanda suka rasu kuma Allah ya bai wa iyalan su juriyar wannan rashi mara misaltuwa.”

 

Kwamandan Hukumar Kiyaye Haɗurra ta Ƙasa (FRSC), reshen Jihar Neja, Mista Kumar Tsukwan, ya shaida wa manema labarai a ranar Litinin cewa dukkan waɗanda abin ya shafa maza ne, kuma da ba a iya tantance motocin da abin ya shafa ba saboda tsananin ƙonewar su.

 

Tsukwan ya bayyana cewa lambar mota ɗaya kacal ce aka iya tantancewa, yayin da ba a gane lambobin sauran ba.

Ya ƙara da cewa lamarin ya faru ne da ƙarfe 4:30 na safe kuma an kai rahoton lamarin ga sashin Lapai na FRSC da ƙarfe 4:40 na safe.

 

Ya ce: “Motar tankar man da ke ɗauke da mai daga Legas zuwa Kano tana gudu sosai, inda ta ƙwace ta faɗi ta kama da wuta yayin da wutar ta shafi wata tirela da ke ɗauke da shanu da mutane tare da wasu motoci biyu a baya. Dukkan motocin guda huɗu sun ƙone ƙurmus.”

“An ruwaito cewa sai da ɗaya daga cikin fasinjojin tirelar da ke ɗauke da mutane da shanun ya ankarar da direban cewa akwai wuta fa a gaban su amma sai direban ya amsa da cewa taya ce kawai ke ƙonewa, kuma da isa wurin tankar da ke ci da wuta, wutar ta kama tirelar da kuma wasu motoci biyu.”

 

A cikin wani ƙarin bayani, Hukumar Ba Da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA) ta ce adadin waɗanda suka mutu ya ƙaru daga 48 da aka bayyana da farko zuwa 59 saboda an gano wasu gawarwaki wajen ci gaba da ceto yayin da ɗaya daga cikin waɗanda abin ya shafa da ya ƙone sosai ya mutu a Cibiyar Kula da Lafiya ta Tarayya da ke Bida.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya
Labarai

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba
Labarai

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci
Labarai

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Next Post
Sin: Ya Kamata Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Da Afirka Ta Kasance Cikin Adalci, Daidaito Kuma A Bayyane

Sin: Ya Kamata Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Da Afirka Ta Kasance Cikin Adalci, Daidaito Kuma A Bayyane

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version