Fasinjoji 15 Sun Bace Yayin Da Mahara Suka Farmaki Mota A Taraba
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fasinjoji 15 Sun Bace Yayin Da Mahara Suka Farmaki Mota A Taraba

bySadiq
2 years ago
Fasinjoji

Akalla fasinjoji 15 da suka hada da mata da yara ne suka bace a wani hari da mahara suka kai wa wata motar kirar bas mai dauke mutane 18 da ta taso daga Zaki/Biam a Jihar Benue zuwa Maihura a Karamar Hukumar Bali ta Jihar Taraba.

Maharan dauke da muggan makamai sun kai wa motar hari a kauyen Gamkwe da ke Maraban-Baisa a Karamar Hukumar Donga a jihar.

  • Barcelona Ta Kai Matakin Kwata Final A Gasar Zakarun Turai Bayan Shekara 4
  • Tinubu Ya Bai Wa Gwamnoni Mako 2 Su Kawo Karshen Matsalar Manoma Da Makiyaya

Direban bas din, Mista Mpuuga Mbaave wanda ya tsallake rijiya da baya, ya zanta da wakilinmu ta wayar tarho, ya ce yana zargin ‘yan banga ne suka kai harin.

“Na yi lodin fasinjoji 18 daga Zaki/Biam, kawai sai na hangi mutane da yawa, na yi zargin cewa wani abu ne ya faru, sai na tsaya amma daya daga cikin fasinjojin ya ce min na tafi amma na ki.

“Da na matsa kusa, sai wasu daga cikin ‘yan bangar suka fara ihu, suna cewa kashe su, su ne suka kashe mambobinmu, sai suka fara saran fasinjojinmu da adduna.

“Sun kwashe mu gaba daya, suka tilasta mana muka kwanta, motata tana kunne da na ga lamarin na neman kacamewa sai fice na bar fasinjojin, shi ma yaron motata ya biyo ni, kuma duk sun sare mu da adda ga jini ko ina a jikinmu, ta haka muka tsira muka bar fasinjojin a can,” in ji Mpuuga.

Shugaban Karamar Hukumar Doonga, Hon. Ezra Voka ya tabbatar wa LEADERSHIP faruwar lamarin ta wayar tarho, inda ya ce tuni ya je dajin da ke kusa da wajen don neman fasinjojin.

“Abokina, ina daji don neman mutanen da suka bace, ba zan iya magana ta yawa ba har sai lokacin da na samu karin bayani daga nan,” in ji Voka.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya
Labarai

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba
Labarai

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci
Labarai

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Next Post
Sojoji Sun Ceto Mutane 10 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Zamfara

Sojoji Sun Ceto Mutane 10 Da 'Yan Bindiga Suka Sace A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version