Firaministan Kasar Sin Ya Ziyarci Yankunan Da Suka Yi Fama Da Bala’in Girgizar Kasa
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Firaministan Kasar Sin Ya Ziyarci Yankunan Da Suka Yi Fama Da Bala’in Girgizar Kasa

byCGTN Hausa
2 years ago
Sin

Firaministan kasar Sin Li Qiang, ya ziyarci yankunan da suka sha fama da girgizar kasa a arewa maso yammacin kasar Sin a jiya Asabar, inda ya yi kira da a dauki dukkanin matakan da suka kamata, wajen kyautata yanayin rayuwar mazauna wuraren.

Li, ya ziyarci kauyuka da dama a gundumar Jishishan dake lardin Gansu, da gundumar Minhe dake lardin Qinghai mai makwaftaka.

  • Tsohon Firaministan Belgium: Ya Dace EU Ta Nuna Matsayar Kanta A Maimakon Kasancewa ‘Yar Koren Amurka
  • MDD Ta Sanar Da Bikin Bazara Na Sin A Matsayin Daya Daga Bukukuwan Da Za A Rika Kiyaye Kimarsu

Yayin ziyarar ta sa ya zanta kai tsaye da mutanen da ibtila’in ya shafa, ya kuma ji yadda ayyukan samar musu matsugunai, da tallafin jin kai, da sake gina wuraren zaman su ke gudana. Kaza lika, ya ce muhimmin abun da ake so a cimma nasarar sa cikin ayyukan jin kai shi ne tabbatar da jama’ar da bala’in ya shafa sun samu muhalli mai kyau mai dumi a wannan lokaci na hunturu.

Firaministan na Sin ya kara jaddada kira ga ma’aikatan jin kai da su kara azamar samar da kayayyakin bukata, da na amfanin yau da kullum ga mazauna wadannan yankuna, tare da gina gidajen wucin gadi cikin sauri ga wadanda ke zaune a tantuna.

Ya kuma ba da umarnin sake duba gine gine, da karfafa wadanda suka kamata, ta yadda mutane za su iya komawa, tare da samun damar sake bude muhimman ababen more rayuwa kamar makarantu da asibitoci.

Da misalin karfe 12 saura minti 1 na daren ranar Litinin din makon jiya ne girgizar kasar mai karfin maki 6.2 ta auku. Kuma ya zuwa ranar Juma’a, adadin wadanda ta hallaka ya kai mutane 148, baya ga mutane 781 da suka jikkata. Kana ibtila’in ya lalata gine gine da dama. (Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?
Daga Birnin Sin

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
Next Post
Sojoji Sun Mikawa Gwamnatin Sokoto Mutane 66 Da Aka Ceto A Jihar 

Sojoji Sun Mikawa Gwamnatin Sokoto Mutane 66 Da Aka Ceto A Jihar 

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version