Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Gaidam Ya Yaba Wa Kungiyoyin Bayar Da Tallafi Ga ‘Yan Gudun Hijira

by
4 years ago
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Daga Muhammad Maitela,

Gwamnan jihar Yobe Alhaji Ibrahim Gaidam ya yaba da tallafin jinkai da kungiyoyi ke bayarwa ga ‘yan gudun hijira a jihar, tare da bayyana cewa akwai bukatar yin aiki tukuru wajen yuwuwar mayar da ‘yan gudun hijirar zuwa yankuanan su na asali, domin su ci gaba gudanar da rayuwa kamar yadda suka saba.

Gaidam ya yi bayyana haka ne a sa’ilin da babban Darakta hukumar bunkasa abinci ta duniya (WFP) a Nijeriya; Misis Myrta Kaulard, ta kai masa ziyara a babban birnin jihar dake Damaturu.

Labarai Masu Nasaba

“Ina Cikin Wani Hali, An Kashe Matata Da Ciki Wata 9 Da Yara 4” —Mijin Matar Da IPOB Suka Kashe

An Karrama Buhari Da Lambar Yabo Kan Kwazonsa Wajen Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa

Ya bayyana cewa dangane da yunkurin da gwamnatin jihar Yobe ta yi a bangaren, hadi da sauran kungiyoyin bayar da agajin gaggawa. Ya ce akwai bukatar a sake zare dantse da kara tallafi wajen saukake wa ‘yan gudun hijirar yanayin rayuwa.

“Wannan kira dangane da sake duba yuwuwar mayar da jama’ar zuwa muhallin su ya zo ne bisa la’akari da irin karin ayyukan jinkai da aka gudanar wa wadanda kuma zasu karfafa gwiwa ga ‘yan gudun hijirar jihar Yobe hadi da wadanda tuni sun koma da zama a cikin garuruwan su na asali.” Inji shi.

Haka kuma, Gaidam ya yaba da kokarin hukumar WFP da ta raba tallafin Mayan abinci ga kananan yara 17,000 domin rage matsalolin karancin abinci mai gina jiki ga yara a jihar. Ya sake nuna farin cikin yadda hukumar ta tallafa da kayan abinci da na noma ga magidanta kimanin 7,000 a kananan hukumomin Gujba da Gulani wadanda suka fi fuskantar matsalar tsaro a jihar.

Bugu da kari kuma, Alhaji Ibrahim Gaidam ya yaba da kokarin yan kwamitin da aka damka wa alhakin kula da sake farfado da yankunan ‘yan gudun hijirar, a karkashin mataimakin gwamnan jihar Alhaji Injiniya Abubakar D Aliyu.

Ya ce gwamnatin jihar Yobe bata taba samun wani koke ko rahoton karkata kayan masarufi da na abinci wanda aka ware domin ‘yan gudun hijira wadanda rikicin Boko Haram ya shafa. Ya ce wannan babban abin alfahari da bugun kirji ne.

ADVERTISEMENT

Misis Kaulard ta ce makasudin zuwan ta a jihar shi ne domin ta samu kafar tattaunawar hadin gwiwa da gwamnatin jihar Yobe domin gudanar da aikin bai daya wajen lalabo tudun dafawa wajen sake farfado da yankunan ‘yan gudun hijirar jihar.

“hukumar bunkasa abinci ta duniya ta ziyarci jihar Yobe domin yin musayar yawu da shawarwari tsakanin ta da gwamnatin jihar Yobe, a bangarorin da suka shafi hada hannu wuri guda wajen farfado da lamurran ‘yan gudun hijira a wannan yanki “. In ji ta.

 

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

‘Yan gudun Hijira 307 Sun Sami Tallafin Filaye, Kayan Gini Da Kudi A Yobe

Next Post

Cikin Shekaru Biyu An Haifi Jarirai 100 A Sansanin ‘Yan Gudun Hijira A Yobe

Labarai Masu Nasaba

“Ina Cikin Wani Hali, An Kashe Matata Da Ciki Wata 9 Da Yara 4” —Mijin Matar Da IPOB Suka Kashe

“Ina Cikin Wani Hali, An Kashe Matata Da Ciki Wata 9 Da Yara 4” —Mijin Matar Da IPOB Suka Kashe

by Leadership Hausa
4 hours ago
0

...

An Karrama Buhari Da Lambar Yabo Kan Kwazonsa Wajen Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa

An Karrama Buhari Da Lambar Yabo Kan Kwazonsa Wajen Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa

by Muhammad Bashir
6 hours ago
0

...

IPOB Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Wata Mata Bahaushiya Da Yaranta 4 A Anambra

IPOB Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Wata Mata Bahaushiya Da Yaranta 4 A Anambra

by Muhammad Bashir
15 hours ago
0

...

Nijeriya Zata Ringa Kashe Miliyan 999 Kullum Wurin Ciyar Da ‘Yan Firamare Miliyan 10

Nijeriya Zata Ringa Kashe Miliyan 999 Kullum Wurin Ciyar Da ‘Yan Firamare Miliyan 10

by
16 hours ago
0

...

Next Post

Cikin Shekaru Biyu An Haifi Jarirai 100 A Sansanin ‘Yan Gudun Hijira A Yobe

Leave Comment

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: