Gamayyar Matasan Arewa A Kudu Ta Yi Tir Da Karuwar Ta’addanci A Arewa
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gamayyar Matasan Arewa A Kudu Ta Yi Tir Da Karuwar Ta’addanci A Arewa

byAbdulrazaq Yahuza
3 years ago
Arewa

Gamayyar Kungiyoyin Matasan Arewa da ke Kudancin Nijeriya a Jihar Legas ta yi Allah wadai da yadda hare-haren ta’addanci suke kara tsamari a yankunan arewa.

Gamayyar wacce ta nuna takaicinta kan lamarin ta bakin shugabanta, Alhaji Ibrahim Ya’u Galadanci, ta bayyana cewa bisa irin ukubar da ake sha, lokaci ya yi da mutanen arewa za su gane ba su da shugabanni masu kishin su, “domin yadda ake kashe mutane tsakanin Katsina, Sakkwato, Zamfara da Kaduna babu ji babu gani kuma an ja baki an yi shuru abin ya wuce hankali. Shin akwai maganar da wasu za su fada nan gaba mu ji su mu yi aiki da su kuwa?”
“Domin kamar tsuntsu ya fi Dan’adam daraja a Nijeriya musamman wanda ya fito daga yankin arewacin kasar, wato su a tunanin shugabaninmu ba mu san abin da muke yi ba ko? A sace mu a dinga yi mana kisan gilla amma ko a jikinsu muna kira da babbar murya ga masu madafan iko na arewacin kasar nan da su yi karatun ta nutsu saboda duk nisan jifa kasa za ta sauko.

  • Jami’an Tsaro Sun Cafke Mutumin Da Ake Zargi Da Laifin Hada Bama-Bamai A Jihar Taraba

“Tun a 1999 ake yakar arewa ana sace dukiyar da Allah ya shimfida a yankin. A bisa wannan ne ma aka kirkiri boko haram da fadar Fulani makiyaya, ga ‘yan kungiyar aware ta kabilar ibo, ga kungiyoyin yarabawa. Duk wadannan kungiyoyin ba su da wani buri ban da kisan mutanen arewa.” In ji gamayyar.

Wakazalika gamayyar ta ce a halin yanzu abin ya zama wa ‘yan arewa gaba-kura-baya-siyaki saboda ana kashe a yankinsu, sannan yankunan da wasunsu suka fita neman abinci ma ana musu barazana, tana mai cewa, “Ba za mu manta da kalaman da Gwannan Ondo ya yi a kan jama’ar arewacin kasar nan wanda ya ce Hausa/Fulani tarihi yana maimaita kansa, su Sardauna, Tafawa Balewa da Murtala Ramat Muhammed duk kisan gilla aka yi musu, Kun manta da wannan? Dan hakka ku canja tunani saboda lokaci ya kusan kure muku.

Wai a ce daga bakin gwamna ne sukutum wannan maganar ta fito kuma babu mai nuna masa yatsa daga arewar, to ina ake so al’ummarmu ta saka kanta?”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya
Rahotonni

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

October 4, 2025
Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin
Rahotonni

Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin

October 3, 2025
Next Post
An Yi Garkuwa Da Matar Shugaban APC Na Karamar Hukumar Magama A Jihar Neja

'Yan Sanda Sun Ceto Matar Shugaban APC Na Jihar Neja Da Aka Sace A Borno

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version