Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

Gamsuwar Al’umnar Gwarzo Da Ayyukan Da Gwamna Ganduje Ke Yi Ta Sa Suka Zabi APC A Zaben Kananan Hukumomi -Baban Gandu

by Muhammad
January 24, 2021
in RAHOTANNI
2 min read
Gwarzo
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Ibrahim Muhammad,

Shugaban hukumar kwashe shara da tsaftar muhalli na jihar Kano Alhaji Abdullahi Ma’azu Gwarzo Baban Gandu ya yaba wa Gwamnan jihar Kano Dokta Abdullahi Umar Ganduje da sauran masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC  saboda tsara abubuwa da tabbatar da gudanar zabe na kananan hukumomi a jihar Kano da jam’iyyar APC ta yi nasara.

Ya ce su a Gwarzo an kai Mayan zabe da wuri kuma wakilan jam’iyyu sun shaida anyi zabe a dukkan mazabu al’umma sun fito suka sake zabar shugaban karamar hukumar Gwarzo  domin ya zarce a karo na Biyu wannan ya nuna yana zaman lafiya da jama’a kuma sun gamsu da mulkinsa na farko bisa yanda aka kada masa kuri’u a Gwarzo.

Ya ce abin da ya jawowa shugaban karamar hukumar nasarar, shi ne zama lafiya da al”umma da irin ayyuka da Gwamnatin APC take tun daga matakin kasa jiha, karamar hukumar da mazabu duk dan siyasa a wannan yanayi da ake ciki dole ya yi wa Allah godiya da jagorori da aka samu a wannan yanayi musamman in aka kalli karamar hukumar Gwarzo kusan dukkaninsu da Gwamnan Kano ya basu madafun iko duk matasa ne.

Alhaji Abdullahi Mu’azu Gwarzo ya yi kira ga al’umma musamman masu mulki a Gwarzo dana  sauran madafu musamman shugaban karamar hukuma da kansiloli da aka zaba su sani nauyi ne Allah ya dora musu kuma kamar yau aka taru aka zabesu kuma idan wa’adinsu ya yi za su sauka in kaje ofishin shugaban karamar hukuma zaka ga sunaye wajen 40 wane ya yi ya sauka wane ma haka kaima wata rana za a zo kanka  ka  sauka  to dole ne  abinda zaka rika tunawa me kayi a baya kuma dukkanin kulawa da tsaro shugaban karamar hukuma Gwarzo yana iya kokarinsa kwarai da gaske, dole a yaba masa, wannan abubuwa yakamata duk.wani shugaba ya tuna Allah zai tambaye su ranar  alkiyama hakkunan al’umma dan haka su rike amana.

SendShareTweetShare
Previous Post

Ziyarar Kwamitin Kasuwar Mile 12 Don Jajanta Wa Manoman Jihar Kano Ya Yi Armashi

Next Post

Cibiyar Nazarin Dimokradiyya Ta Jami’ar Bayero Ta Nuna Rashin Gamsuwa Da Yadda Ake Gwamnoni Ke Gusanar Da Zaben Kananan Hukumomi

RelatedPosts

Tuhumar Malam Abduljabbar Za A Yi, Ba Mukabala Da Shi Ba– Sheikh Khalil

by Sulaiman Ibrahim
1 day ago
0

Daga Nasir S. Gwangwazo, Abuja Shugaban Majalisar Malamai na Shiyyar...

ISWAP

Boko Haram Ta Yi Garkuwa Da Ma’aikatan Jinkai Bakwai A Dikwa

by Sulaiman Ibrahim
1 day ago
0

Daga Muhammad Maitela, Maiduguri A harin bayan nan da mayakan...

Makanike

Shari’ar Gonaki: Kotu Ta Aike Wa Rundunar Soja Da Ma’aikarar Shari’a Sammaci

by Sulaiman Ibrahim
1 day ago
0

Daga Isa Abdullahi Gidan ‘Bakko, Zariya Kotun daukaka kara dake...

Next Post
Jami'ar Bayero

Cibiyar Nazarin Dimokradiyya Ta Jami'ar Bayero Ta Nuna Rashin Gamsuwa Da Yadda Ake Gwamnoni Ke Gusanar Da Zaben Kananan Hukumomi

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version