Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Ganduje Ya Kai Ziyarar Bazata Gidan Shekarau Kan Ya Amsa Gayyatar Buhari Ta Sulhu

Jirgi na dakon Jiran daukar Sanata Shekarau da Gwamna Ganduje zuwa fadar Sugaban kasa don Sulhunta su.

by Leadership Hausa
3 days ago
in SIYASA
2 min read
Ganduje Ya Kai Ziyarar Bazata Gidan Shekarau Kan Ya Amsa Gayyatar Buhari Ta Sulhu
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

An yammacin ranar Juma’ar nan shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya aiko da jirgi sukutum daga Abuja tare da umarnin lallai a lallashi Sanata Shekarau ya dakatar da fiacewa daga Jam’iyyar APC.

Tunda farko dai gwamnan ya aike da wata tawagar Jami’an gwamnatin Kano da ta hada da Kwamishinan yada labaran Jihar, Muhammad Garba tare da shugaban masu rinjaye a majalisar wakilan Nijeriya Alasan Ado Doguwa kan su je gidan Shekarau su lallashe shi su kuma isar masa da sakon shugaban kasa.

  • 2023: Shekarau Ya Yi Watsi Da Bukatar Gawuna Ta Hana Shi Ficewa Daga APC Zuwa NNPP
  • 2023: Ban Gama Yanke Shawarar Ficewa Daga APC Ba Tukunna —Sanata Shekarau

Sai dai Sanata Shekarau din ya yi watsi da bukatar gayyatar ta shugaban kasar cewa ba zai je Abuja don tattaunawa kan batun sulhu da tsagin na su Gandujen ba.

https://hausa.leadership.ng/wp-content/uploads/2022/05/VID-20220513-WA0011.mp4

Bayan ficewar tawagar gwamnatin daga gidan Shekarau ba jimawa kwatsam sai suka dawo gidan Shekarau da Gwamna Ganduje suka kuma bukaci ganawa da Sanata Shekarau kan ya amsa gayyatar zuwa sulhun a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Majiyarmu daga gidan Sanata Shekarau din ta ce Ganduje da Shekarau sun saka labule sun tattauna na tsawon mintuna 20, sai daga bisani ya fito daga gidan zuwa fadar gwamnatin Kano.

Wani makusancin Sanata Shekarau ya shaida mana cewa zai gana da ‘yan kwamatinsa gabanin yanke hukunci amsa gayyatar sulhun zuwa Abuja don kawo karshen sa-toka-sa-katsin da ake bugawa a Jam’iyyar APC ta Jihar Kano.

Labarai Masu Nasaba

2023: Ganduje Ya Farauto Ciyaman 1 Da Dan Majalisar Da Suka Koma NNPP Zuwa APC

2023 Siyasar Kano: Ganduje Ya Janye Takararsa Ta Sanata Ya Barwa Sanata Barau

Mun samu labarin cewa tun misalin karfe 05:30 na yamma aka turo jirgi daga Abuja kan ya dauki Sanata Shekarau da Gwamna Ganduje don ganawa da Ganduje da shugaban kasa kan sulhunta bangarori biyun da suke tafka rikicin siyasar cikin gida a Jam’iyyar APC ta Jihar Kano.

Majiyarmu ta ce tuni Sanata Shekarau din ya shiga ganawa da magoya bayansa kan bukatar ta sulhun da kuma batun sauya sheka zuwa Jam’iyyar NNPP ta Sanata Rabi’u Kwankwaso da ake saran gobe Asabar zai aiyana shiga Jam’iyyar.

Da daren yau Juma’a ake saran Sanata Rabi’u Kwankwaso zai yi wata ganawar sirri da Sanata Shekarau a gidansa da ke unguwar Mundubawa cikin karamar hukumar Nassarawa.

Abun tambayar anan shin Sanata Shekarau zai amsa batun sulhun rikicin siyasarsa da APC ko zai gana da Kwankwaso kan yuyuwar aiyana shigarsa Jam’iyyar NNPP?

Ku ci gaba da kasancewa tare da mu don jin halin da ake ciki kan wannan batu.

Like this:

Like Loading...
Tags: APCGandujeKanoNNPPShekarau
SendShareTweetShare
Previous Post

Hajojin Habasha Dake Shiga Kasar Sin Na Karuwa In Ji Jakadan Sin A Kasar

Next Post

Ministan Kwadago Ya Janye Daga Takarar Shugaban

Labarai Masu Nasaba

2023: Ganduje Ya Farauto Ciyaman 1 Da Dan Majalisar Da Suka Koma NNPP Zuwa APC

2023: Ganduje Ya Farauto Ciyaman 1 Da Dan Majalisar Da Suka Koma NNPP Zuwa APC

by Leadership Hausa
4 hours ago
0

...

2023 Siyasar Kano: Ganduje Ya Janye Takararsa Ta Sanata Ya Barwa Sanata Barau

2023 Siyasar Kano: Ganduje Ya Janye Takararsa Ta Sanata Ya Barwa Sanata Barau

by Leadership Hausa
5 hours ago
0

...

2023: “Koda Yaushe Za A Ganmu Tare Da Kwankwaso, Za Mu Yi Aiki Da Juna” —Shekarau

2023: “Koda Yaushe Za A Ganmu Tare Da Kwankwaso, Za Mu Yi Aiki Da Juna” —Shekarau

by Leadership Hausa
14 hours ago
0

...

Lokaci Ya Yi Da Matasa Za Su Jagoranci Nijeriya —Hon. Amale

Lokaci Ya Yi Da Matasa Za Su Jagoranci Nijeriya —Hon. Amale

by Ahmed Muh'd Dan'Asabe
19 hours ago
0

...

Next Post
Ministan Kwadago Ya Janye Daga Takarar Shugaban Kasa

Ministan Kwadago Ya Janye Daga Takarar Shugaban

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
 

Loading Comments...
 

    %d bloggers like this: