Abdullahi Muhammad Sheka">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

Ganduje Ya Nada ‘Yan Kwamitin Gudanarwar Sabbin Asibitocin Kwararru Na Kano

by Abdullahi Muhammad Sheka
November 25, 2020
in RIGAR 'YANCI
2 min read
Gwamnatin Kano
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Gwamnan Jihar Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya amince da nadin shugaban kwamitin gudanarwar asibitocin nan biyu na kwararru tare da mambobinsu.

Jawabin haka na kunshe cikin jawabin da babban daraktan yada labaran Gwamnan Jihar Kano Abba Anwar ya rattabawa hannu kuma aka rabawa manema labarai a Kano wanda kuma nadin ya fara aiki nan take.

samndaads

A cewar Gwamna Ganduje an yi wannan nadi ne bisa cancanta, don haka sai ya bukace su da a ko da yaushe su kasance masu yiwa Jihar Kano hidima a farko kafin komai. Kamar yadda yake cikin kunshin dokokin gudanar da harkokin asibitocin biyu.

“Ku tabbatar da ganin kun gudanar da ayyukanku yadda ya kamata, tare da kulawa da matsayin wadannan asibitoci. Wannan Gwamnati na baiwa harkokin lafiya kulawa ta musamman, don haka ku tabbatar da ganin ana tafiya kamar yadda tsarin yake a duniya baki daya,” inji shi.

Wadanda aka nada din sun hada da Prof Yusuf D. Sabo a matsayin shugaba, Dr Hadiza Ashiru matsayin babbar jami’a, Dr Abdullahi Kauranmata wakilin ma’aikatar lafiya, Zahraddeen Lawan wakilin ma’aikatara kudi da Eng. Murtala A. Garba wakili daga ma’ aikatar kiyaye ka’idojin aiki.

Sauran su ne Hajiya Bilkisu Maimota, wakiliya daga ofishin sakataren Gwamnatin Jihar Kano, Hajiya Halima Ali Aware wakiliya daga ma’aikatar zuba jari da kadarori Gwamnati, Hajiya Hafsat Kolo Wakiliyar kungiyoyi masu zaman kansu,, Alhaji Kabiru Nassarawa wakilin kamfanoni masu zaman kansu, Sanusi Ali Sadik daga ANAN/ICAN reshen JiharKano da Madam Comfort Onwuegbuna da ke wakilta kungiyoyin mata.

Gwamna Ganduje ya bukace su da ako da yaushe yi duk mai yiwuwa domin kara inganta hrkokin lafiya a Jihar Kano. “Sannan ku taimakawa wannan Gwamnatin JIhar Kano domin rike kambunta na Jihar da ke sahun gaba a fadin kasarnan wajen samar da ingantaccen tsarin kiwon lafiya.”

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Kungiyar HLWA Ta Bukaci Gwamnatoci Su Bai Wa Ilimin Mata Fifiko

Next Post

Gwamnan Zamfara Ya Sake Kubutur Da Mutane 11 Daga Masu Garkuwa

RelatedPosts

Ebonyi

Kwamishinan ’Yan Sandan Ebonyi Ya Kama Hadiman Gwamnan Jihar Biyu Da Shugaban Karamar Hukuma

by Abdullahi Muhammad Sheka
14 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Rundunar 'yan sanda ta kama wasu...

Direbobi

Bakwai Sun Mutu Da Yawa Sun Jikkata A Rikicin Shugabancin Kungiyar Direbobi

by Abdullahi Muhammad Sheka
14 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, A kalla mutane bakwai ne suka...

Takalmi

Mata Ta Rafka Wa Mijinta Tsinin Dunduniyar Takalmi Ya Mutu

by Abdullahi Muhammad Sheka
14 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Wata mata da ba a bayyana...

Next Post
APC Zuwa PDP

Gwamnan Zamfara Ya Sake Kubutur Da Mutane 11 Daga Masu Garkuwa

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version