Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home RIGAR 'YANCI

Ganduje Ya Ware Naira Biliyan Tara Don Gina Gadar Muhammadu Buhari

by Sulaiman Ibrahim
March 31, 2021
in RIGAR 'YANCI
1 min read
Ganduje Ya Ware Naira Biliyan Tara Don Gina Gadar Muhammadu Buhari
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, Kano

Majalisar zartarwa ta Jihar Kano ta amince da kashe Naira biliyaon kusan tara (N8, 980, 303, 460.63) domin gina gada wadda ake sa ran sawa sunan Shugaban kasa Muhammadu Buhari wadda ke kan Titin Maiduguri da ke ƙwaryar birnin na Kano.
Majalisar ta amince da kashe kudin ne jim kadan bayan kammala zamanta na mako-mako a dakin taro na Africa House da ke fadar Gwamnatin Jihar Kano.
Kwamishinan Yada Labarai Malam Muhammad Garba ya ce wannan yunkuri na cikin burin Gwamnatin Dakata Abdullahi Umar Ganduje na gina tituna da hanyoyi domin mayar da Kano “hamshakin birni” da kuma habaka harkokin kasuwanci.
A cewarsa: “Kasancewar Kano birni mai tasowa kuma cibiyar kasuwanci a Nijeriya, Kano na samun karuwar ‘yan kasuwa da ke shigowa, abin da ya sa ake bukatar sake tsarawa tare da habaka tituna don su iya daukar masu zirga-zirga a cikinsa.”
A makon da ya gabata ne tsohon Gwamna kuma jagoran adawa a Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya soki aikin gadar, yana mai cewa “mutanen Kano sun fi bukatar ilimi” ba gada ba.
Kazalika, kwamishinan ya ce majalisar ta amince da kashe Naira Miliyon 44,300,000 domin yi wa Kwalejin Harkokin Noma ta Audu Bako da ke karamar Hukumar Dambatta gyare gyare.

SendShareTweetShare
Previous Post

Majalisar Dokokin Katsina Ta Bukaci A Gyara Hanyar Burji A Bakori

Next Post

Muna Addu’ar APC Ta Shekara 32 A Mulki – Sarkin Daura

RelatedPosts

Zamfara

Gwamnatin Jihar Zamfara Ta Tabbatar Da Kama  Wasu Sojoji Masu Hulda Da ‘Yan Ta’adda

by Muhammad
4 days ago
0

Daga Hussaini Yero, Gwamnatin jihar Zamfara ta tabbatar da rahotan...

Kansila Mai Mataimaka 18 Ya Sadaukar Da Albashinsa Na Farko

by Sulaiman Ibrahim
3 weeks ago
0

Daga Abdullahi Muh’d, Kano Shugaban Gidauniyar ‘Charity’ mai rajin tallafa...

APC

Sanata Al-Makura Ya Cancanci Rike Kujerar Shugabancin APC, Inji Gwamna Sule

by Muhammad
3 weeks ago
0

Daga Zubairu M Lawal, A yayin da uwar jam'iyyar APC...

Next Post
Muna Addu’ar APC Ta Shekara 32 A Mulki – Sarkin Daura

Muna Addu’ar APC Ta Shekara 32 A Mulki – Sarkin Daura

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version