Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Gara Da APC Ta Hana Obaseki Takara – Ganduje

by
2 years ago
in LABARAI
1 min read
Kasa
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Gwamnan Jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya ce jam’iyyarsu ta APC ta yi daidai wajen hana takwaransa na Jihar Edo, Godwin Obaseki, izinin sake takara a zabe mai zuwa.

Gwamnan Kanon ya bayyana hakan ne a wata ganawa da ya yi da manema labarai a fadar gwamnatin jihar ranar Litinin.

Ganduje ya ce, jam’iyyar ta bi matakan da su ka dace wajen daukar matakin, kuma su yanzu abinda ke gabansu shi ne, samun nasarar zaben da sabon dan takarar da jam’iyyar za ta tsayar.

Labarai Masu Nasaba

Zargin Sauyin Sheka Yasa Majalisar Dokokin Kano Ta Dage Zamanta Na Ranar Litinin

Deborah: Kungiyar Gwamnonin Arewa Ta Bukaci A Zauna Lafiya

Gwamnan ya ce, Jihar Kano za ta yi iya bakin kokarinta wajen ganin Jam’iyyar APC ta lashe kujerar gwamnan Jihar Edo, saboda yadda a ka bi matakan da su ka dace daki-daki.

Amma a nashi bangaren, Gwamnan Jihar Ribers, Nyesome Wike, na jam’iyyar PDP, ya cacaki shugabannin Jam’iyyar APC kan matakin da su ka dauka na haramta wa Gwamna Obaseki takara, inda ya ce, zai yi iya bakin kokarinsa wajen ganin gwamnan ya lashe zabe mai zuwa.

Rahotanni sun ce PDP na zawarcin Obaseki, amma gwamnan ya ce, ba zai yanke hukunci kan makomarsa ba har sai ya gana da Shugaban Kasa Muhammadu Buhari nan gaba.

Sai dai kuma a jiya gwamnan na Edo ya bayar da sanarwar ficewarsa daga APC din bayan ya ziyarci Fadar Shugaban Kasar, duk da cewa, rahotanni sun tabbatar da cewa, bai gana da Shugaba Buhari ba.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Ka Iya Bakinka Kan Ango Abdullahi – Kashedin AYCF Ga Adesina

Next Post

Ki Yaki Matsalar Tsaro Kamar Yadda Ki Ke Wa Korona – Reb Bukisin Ga Gwamnati

Labarai Masu Nasaba

Zargin Sauyin Sheka Yasa Majalisar Dokokin Kano Ta Dage Zamanta Na Ranar Litinin

Zargin Sauyin Sheka Yasa Majalisar Dokokin Kano Ta Dage Zamanta Na Ranar Litinin

by
12 hours ago
0

...

Deborah: Kungiyar Gwamnonin Arewa Ta Bukaci A Zauna Lafiya

Deborah: Kungiyar Gwamnonin Arewa Ta Bukaci A Zauna Lafiya

by
15 hours ago
0

...

Ganduje Ya Umurci Bala Ya Kula Da Ofishin Shugaban Ma’aikata Fadar Gwamnatin Kano

Ganduje Ya Umurci Bala Ya Kula Da Ofishin Shugaban Ma’aikata Fadar Gwamnatin Kano

by
20 hours ago
0

...

Deborah: Matasan Musulmai Ba Su Kona Min Gidana Ba —Bishop Kukah

Deborah: Matasan Musulmai Ba Su Kona Min Gidana Ba —Bishop Kukah

by Abubakar Abba
22 hours ago
0

...

Next Post
Ki Yaki Matsalar Tsaro Kamar Yadda Ki Ke Wa Korona – Reb Bukisin Ga Gwamnati

Ki Yaki Matsalar Tsaro Kamar Yadda Ki Ke Wa Korona – Reb Bukisin Ga Gwamnati

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: