Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Gargaɗin Ngozi Ga Hukumar IMF: Ku Bi Sannu Da ’Yan Wankiya A Nijeriya

by Tayo Adelaja
October 17, 2017
in LABARAI, MANYAN LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

 Daga Sulaiman Bala Idris

A ranar Lahadin makon da ya gabata, tsohuwar ministar kuɗi kuma shugabar hukumar GAƁI, Dakta Ngozi Okonjo-Iweala, ta gargaɗi ga Hukumar Bada Tallafi ta Duniya (IMF) da wasu cibiyoyin duniya da su riƙa taka-tsantsan da ƙungiyoyi masu zaman kansu waɗanda ke iƙirarin faɗa da cin hanci da rashawa a faɗin tarayyar Nijeriya.

samndaads

Ta bayyana cewa, da yawan waɗannan ƙungiyoyi masu iƙirarin yaƙi da cin hanci a Nijeriya, suna fake wa da guzuma ne domin su harbi karsana. Kuma karnukan farauta ne na mutanen da ke cikin gwamnati.

Okonjo-Iweala ta bayyana haka ne Birnin Washington DC, dake ƙasar Amurka a wurin taron shekara-shekara wanda Babban Bankin Duniya da Hukumar Bada Tallafi suke shirya wa, mai taken ‘Yaƙi da Cin hanci da rashawa’.

“Duk yadda za ku dage, babu wani abu da za ku iya taɓuka wa daga waje. Kuna buƙatar sanin haƙiƙanin cibiya ko ƙungiya da mutanen da ke cikinta, domin fahimtar waɗanda a shirye suke su yi wannan aikin tsakaninsu da Allah, sai a taimaka musu.

“Saboda ni na san tsiyar ƙasa ta Nijeriya. A maimakon ku haɗu da ƙungiyoyi masu zaman kansu, za ku faɗa tarkon ‘yan wankiya ne, ma’ana ƙungiyoyi masu zaman wasu ɗaiɗaikun al’umma.

“Sannan kuma dole ku sani cewa, waɗannan ‘yan wankiyan ba ƙaramin wayo suke da shi ba. Ga su da dabaru iri-iri. Ba wai kawai sakaka suke gabatar da lamurransu ba. Suna ƙirƙirar ƙungiyoyi ne saboda su zamar musu mafaka. Don su ci gaba da yi wa al’umma kan ta waye.

“Ana buƙatar takatsantsan da kula. Sai an natsu za a gane ƙungiyoyin ƙwarai. Sannan muna da ƙungiyoyin na gaske, masu yin yaƙi da cin hanci da rashawa tsakaninsu da Allah. Ya kamata ku san waɗanda ke shirya muku ƙarairayi da waɗanda ke faɗin gaskiya a lamurransu.” Inji ta

SendShareTweetShare
Previous Post

Uwar Jam’iyyar PDP Ta Ziyarci IBB: Ya Gargaɗi ‘yan Siyasa Kan Zaman Lafiya

Next Post

Badaƙalar NNPC: Ba A Taɓa Mazambaciyar Gwamnati Kamar Ta Buhari Ba –Lamiɗo

RelatedPosts

Ibrahim Musa Dankwairo: Sarakuna Sun Kyale Makadan Fada A Lalace

Ibrahim Musa Dankwairo: Sarakuna Sun Kyale Makadan Fada A Lalace

by Sulaiman Ibrahim
15 hours ago
0

Makadan Fada na yanzu sun shiga wani hali mai ban...

Yanzu-yanzu: Gwamnan Gombe Ya Nada Sabon Mai Tangale

Yanzu-yanzu: Gwamnan Gombe Ya Nada Sabon Mai Tangale

by Muhammad
17 hours ago
0

Daga Khalid Idris Doya, Gwamnan jihar Gombe, Alhaji Muhammad Inuwa...

jana'izar

‘Yan Majalisa Biyu Sun Fice Daga APC A Bauchi

by Muhammad
18 hours ago
0

Daga Khalid Idris Doya, 'Yan Majalisun Dokokin jihar Bauchi biyu...

Next Post

Badaƙalar NNPC: Ba A Taɓa Mazambaciyar Gwamnati Kamar Ta Buhari Ba –Lamiɗo

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version