Garin Kwakin Da Ake Sarrafawa A Yankin Ugep Ya Janyo Takaddama
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Garin Kwakin Da Ake Sarrafawa A Yankin Ugep Ya Janyo Takaddama

byAbubakar Abba
3 years ago
Garin Kwaki

Cacar-baki ta barke tsakanin masu ruwa da tsaki a fannin sarrafa rogo zuwa garin kwaki da ake kira da Ugep ‘Garri’. Ugep ‘Garri’, ana sarrafa shi ne a garin Ugep da ke a karamar hukumar Yakur a jihar Koros Ribas.

Musayar yawun a tsakanin masu ruwa da tsakanin a fannin ta kaure ne biyo bayan furucin da shugaban kungiyar masu sarrafa Garin Kwaki reshen jihar (CGAN), Mista Augustine Okua ya yi na gargadin al’ummar da ke Kudancin Nijeriya, da na kasa baki daya ma cewa su guji shan Garin Kwakin da ake sarrafa wa a yankin na Ugep.

  • Mutane 8 Sun Mutu, 2 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kogi 
  • Harin Jirgin Kaduna-Abuja: Hukumar Jiragen Kasa Ta Yi Asarar Miliyan 53 A Cikin Watanni 5

A wata hira da Augustine ya yi zargin cewa, garin shan zai iya shafar kiwon lafiyar jama’ar da suka sha shi, ganin cewa, wasu masu sarrafa rogo a yankin zuwa Garin Kwaki suna yi a cikin gaggawa ba tare sun bar rogon ya gama tsanewa ba don kawai su samu kudi da wuri.

Ya ce, Gari na dauke da sanadarin cyanide masu nauyin gaske wanda kuma zai iya shafar kiwon lafiyar wanda ya yi amfani da shi ko kuma ya jawo mutuwar wanda ya yi amfani da su, inda ya yi nuni da cewa, akalla ya fi da cewa a bar rogon ya kai kwana uku kafin a fara soya shi don mayar da shi gari.

Sai dai, wannan kalaman na Augustine, bai yi wa sauran masu ruwa da tsaki a fannin daga ke a jihar dadi ba, inda wasun su suka mayar masa da kakkausar martani.

Wasu daga cikinsu, sun ce, Augustine ya yi furucin ne saboda gonarsa ta noman Rogo karamace, inda a yanzu ya ke son zama mai sarrafa gari, hakan kuma ya sa yake son ya tsorata ‘ yan Nijeriya da sauran masu yin amfani da shi da ake sarrafa wa a garin na Ugep.

Cif Okoi Obono-Obla, tsohon mai bai wa shugaba Muhammadu Buhari shawara kuma basarake a garin na Ugep, shi ma ya soki furucin na Augustine, inda ya ce Augustine na kawai son bata wa garin suna ne da kuma son hana wa samun Garin karbuwa a gun jama’a.

Ya ce, kamata ya yi Augustine a matsayin san a shugaban kungiyar ya dinga kare ‘yancin masu sarrafa shi zuwa gari, amma ba kawai ya shiga kafafen yada labarai ya yin batacin kan Garin da ake sarrafa wa a garin ba.

Ya kara da cewa, kamata ya yi kafin ya yi furucin ya faga da jin ra’ayoyin ta alummar Ugep da kuma sauran masu sarrafa rogon.

“Kamata ya yi Augustine a matsayin san a shugaban kungiyar ya dinga kare ‘yancin masu sarrafa rogo zuwa zuwa gari, amma ba kawai ya shiga kafafen yada labarai ya yin batacin kan garin da ake sarrafa wa a garin ba”.

Ya yi nuni da cewa, garin da ake sarrafa wa a yankin shi ne ya fi kyau a daukacin fadin kasar nan.

Shi ma Yariman yankin Mkpani Oka Ibor ya sanar da cewa, furucin na Augustine son nuna gawawar alummar garin ne da kuma bata masu suna, musamman manyan masu sarrfara rogo zuwa gari a garin.

Sai dai, wani masani a fannin sarrafa rogo zuwa gari a yankin Mike Kit Oka ya sanar da cewa, rogo na dauke da sanadarin cyanide kadan ne, sabanin sanadarin na cyanide da ke jikin sauran amfanin gona.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

October 3, 2025
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

October 3, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

September 27, 2025
Next Post
Csaba Korosi: Sin Ta Zamo Babbar Garkuwa Ga Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya Na MDD

Csaba Korosi: Sin Ta Zamo Babbar Garkuwa Ga Ayyukan Wanzar Da Zaman Lafiya Na MDD

LABARAI MASU NASABA

…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version