Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home WASANNI

Gasar Firimiya Abar Tsoro Ce –Tuchel

by Muhammad
April 5, 2021
in WASANNI
2 min read
Tuchel
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Kociyan kungiyar kwallon kafa ta Chelsea, Thomas Tuchel, ya bayyana cewa gasar firimiyar kasar Ingila bata da tabbas kuma abar tsoro ce saboda haka yana fatan kungiyarsa za ta farfado daga rashin nasarar da ta yi a wasan ranar Asabar.

A karon farko an doke mai koyarwa Thomas Tuchel a matsayinsa na kocin kungiyar kwallon kafa ta Chelsea bayan kungiyar kwallon kafa ta West Bromwich Albion ta yi raga-raga da kungiyar da ci 5-2 a filin wasa na Stamford Bridge dake birnin London.

Chelsea ta kare wasan ne da ‘yan wasa 10 bayan an bai wa dan wasanta na baya, Thiago Silba jan kati sakamakon kama shi da aka yi da laifi har sau biyu kuma ana bashi katin gargadi.

Tuchel ya buga wasanni 14 ba a doke shi ba a dukkanin wasannin da ya buga a kungiyar, bayan Chelsea ta kori tsohon kociyanta, Frank Lampard a watan Janairun wannan shekarar da muke ciki.

Dan wasan Chelsea Christian Pulisic ne ya fara zira kwallo a raga, kafin a bai wa Thiago jan kati sannan ana dab da zuwa hutun rabin lokaci dan wasan West Brom Albion Matheus Pereira ya ci kwallaye biyu, ya zama ana nasara akan Chelsea da ci 1-2.

Mbaye Diagne ya ci wa West Brom kwallo ta uku yayin da kuma Callum Robinson ya rufe da sauran kwallayen a ragar Chelsea wanda hakan ya sa kociyan kungiyar, Sam Allardyce ya bayyana cewa wasan ya bashi mamaki.

Sakamakon wasan wani kalubale ne ga fafutukar da kungiyar kwallon kafa ta Chelsea take na kare gasar a cikin jerin kungiyoyin hudun farko domin samun gurbin zuwa gasar cin kofin zakarun Turai na kakar wasa mai zuwa.

Wannan ne karon farko da aka ci Chelsea kwallaye biyar tun shekarar 2011 da Arsenal ta zazzaga mata kwallayen kuma Thiago Silba mai shekara 36 a duniya shi ne dan wasa mafi tsufa da aka bai wa jan kati a kungiyar tun John Terry a shekarar 2016.

SendShareTweetShare
Previous Post

Anci Tarar Kungiyar Katsina United

Next Post

Haaland Ya San Kungiyar Da Yake Son Zuwa

RelatedPosts

Leicester

Leceister City Ta Je Wasan Karshe A Kofin FA Bayan Shekara 52

by Muhammad
2 hours ago
0

Kungiyar kwallon kafa ta Leicester City ta kai wasan karshe...

Juventus Ta Sake Samun Koma Baya A Siriya A  

by Muhammad
2 hours ago
0

Kungiyar kwallon kafa ta Juventus ta sake samun koma baya...

Getafe

Akwai Gajiya A Jikin ‘Yan Wasana Lokacin Fafatawa Da Getafe – Zidane

by Muhammad
2 hours ago
0

Kociyan kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid, Zinadine Zidane, ya...

Next Post
Haaland

Haaland Ya San Kungiyar Da Yake Son Zuwa

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version