Abdullahi Muhammad Sheka">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

Gatan Sakatariyar Da Ake Kwana 30 Ba A Shige Ta Ba Ya Zo – Alwashin Shugaban Karamar Hukumar Kunchi

by Abdullahi Muhammad Sheka
February 17, 2021
in RIGAR 'YANCI
2 min read
Gatan Sakatariyar Da Ake Kwana 30 Ba A Shige Ta Ba Ya Zo – Alwashin Shugaban Karamar Hukumar Kunchi
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Shugaban karamar Hukumar Kunchi Alhaji Aminu Idi Shuwaki ya bayyana aniyarsa na Sake fasalin Yadda aiki ke gudana a karamar Hukumar ta Kunchi, musamman batun zuwa aiki akan lokaci. Yace hankali na ya tashi kwarai da gaske ganin halin da sakatariyar karamar Hukumar Kunchi ke ciki. Wannan tasa yau Lahadi muka hallara a sakatariyar karamar Hukumar domin gudanar da aikin tsaftace sakatariyar.

Shugaban na wannan jawabi ne alokacin aikin tsaftace sakatariyar inda shugaban ya tabbatar da aniyarsa na sake fasalin tsarin gudanar da ayyuka da kuma tabbatar da ganin kowa na zuwa bakin aiki. “Ba zan amince da fashin zuwa aiki ba, kuma zamu sa kafar wando daya da duk wanda ke kokarin kassara mana aniyar mu ta sabunta fasalin karamar Hukumar Kunchi.
Alhaji Aminu Idi Shuwaki ya ci gaba da cewa, zan yi aiki tare da duk wanda zai taimaka mana wajen aiwatar da sabon salon Jagorancin da wannan Shugabanci zai ci gaba da aiwatarwa. Zamu tabbatar da inganta harkar samar da kudaden shiga, wanda hakan zai bamu damar kwararawa a al’ummar Kunchi ayyukan raya kasa.
Aminu Shuwaki yace ina da kyakkyawan yakinin kansilolina suna sane da halin da wannan karamar Hukuma ke ciki, kuma mun shigo da kyakkyawar niyya wanda ina tabbatarwa da al’ummar Kunchi ba zamu basu kunya ba. Saboda haka sai shugaban ya bukaci hadin kan jama’a, musamman Malamai da Sarakuna iyayen kasa.
Idan ba a manta ba mako biyu da suka gabata Wakilin Jaridar LEADERSHIP Ayau ya yi tattaki kafa da kafa har zuwa karamar Hukumar ta Kunchi inda muka dan tsakuro kadan daga cikin Matsalolin dake addabar yankin, musamman halin da sakatariyar karamar Hukumar Kunchi wanda wakilin leadership Ayau ta ji ta bakin wani wanda ya bukaci a sakaya sunansa, wanda ya koka bisa yadda ake kwashe wata guda ba tare da bude sakatariyar karamar Hukumar ba.
Yanzu abinda ake jira a gani shi ne yadda ma’aikatan karamar Hukumar Kunchi ke yin kunnen kashi da batun zuwa wurin aiki, sannan Suma masu rike da madafun ikon wadanda ake zargin na yin fuskar shanu wajen kin kwana a yankin.

samndaads
SendShareTweetShare
Previous Post

UNICEF Ta Yi Kwaskwarima Wa Cibiyoyin Lafiya 104 A Bauchi

Next Post

Tallafin Mai Na Lakume Naira Biliyan 11.2 Duk Mako – Bincike

RelatedPosts

Dakarun Tsaro Sun Dakatar Da Aiki A Yankin Orlu Na Jihar Imo

by Abdullahi Muhammad Sheka
6 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, A wani labarin kuma, Dakarun sun...

EFCC

EFCC Ta Cafke Mutum Tara Da Zargin Kutse A Yanar Gizo

by Abdullahi Muhammad Sheka
6 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Jami'an hukumar yaki da cin hanci...

Soja

’Yan Sanda Sun Cafke Korarren Soja Yana Fashi

by Abdullahi Muhammad Sheka
6 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Wani matashi dan shekaru 27 da...

Next Post
Cinikin Fetur Da Gas

Tallafin Mai Na Lakume Naira Biliyan 11.2 Duk Mako – Bincike

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version