Gidauniyar Dangote Da Gwamnatin Kano Za Su Yi Yaki Da Cutar Tamowa
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gidauniyar Dangote Da Gwamnatin Kano Za Su Yi Yaki Da Cutar Tamowa

byKhalid Idris Doya
3 years ago
Tamowa

Gidauniyar Aliko Dangote da hadin guiwar Gwamnatin jihar Kano, asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) tare da kuma gidauniyar Bill and Melinda Gates sun rabba hannun yarjejeniyar fahimtar juna domin yin aiki tare wajen yaki da cutar Tamowa da yara ke fama da shi sakamakon karancin samun abinci mai gina jiki a jihar Kano.

Baya ga bangaren kula da cutar Tamowar, bangarorin za kuma su taimaka wajen inganta kiwon lafiya a jihar tare da kula da yin rigakafi a kai a kai domin kyautata kiwon lafiya musamman na yara da mata.

  • Manoma Sun Koka Kan Hauhawar Farashin Takin Zamani

Jimkadan bayan rabbata hannun a ranar Laraba da ya gudana a fadar Gwamnatin jihar Kano, babban darakta mai cikakken iko na gidauniyar Dangote, Zouera Yousefou, ta taya Gwamnatin jihar Kano murnar kawowa wannan matakin da kuma irin nasarorin da aka samu tun lokacin da suka fara sanya hannun yarjejeniya na farko a 2013 da na biyu a 2017 har zuwa yanzu da suka sake sanya hannu a mataki na uku.

Misis Yousefou ta kuma jinjina wa Gwamnatin Kano din bisa ririta kudaden da aka ware na rigakafi kan hakan ya ce jihar ta samu karin kaso domin kara mata azama kan wannan fannin.

MD/CEO ta kuma kara da cewa bangarorin abokan jeren sun samu nasarori sosai wajen rage kaifin mace-macen mata masu juna biyu da yara a jihar.

Ta ce jami’ansu na sanya ido domin ganin ana tafiyar da lamura yadda suka kamata. Ta nemi sarakunan gargajiya da su kara himma wajen fadakar da al’ummar su muhimmancin kiwon lafiya da amsar rigakafi, abinci mai gina jiki, kula da mata masu juna biyu da sauran bangarorin lafiya.

Ta bada tabbacin gidauniyar nasu na cigaba da taimakawa a fannin kiwon lafiya musamman na yara da mata.

A nashi jawabin, gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya ce jihar ta samu nasarori masu tarin yawa a bangaren kula da lafiyar al’umma.

A cewarsa, gwamnatinsa ba ta wasa sako-sako da harkar kiwon lafiya a kowani lokaci ta hanyar inganta kanana da manyan asibitin kula da lafiya tare da samar da wadatatun ma’aikatan da za su kula da su.

Ganduje ya ce hatta sanya hannun yarjejeniyar na nuni da himmatuwar Gwamnatin ne a bangaren kiwon lafiya.

Ya tabbatar da cewa jihar da ta kula da tallafin da ta samu daga abokan jere domin cimma manufofin da aka sanya a gaba. Sai ya gode musu bisa hakan tare da basu tabbacin kokarin gwamanti a kan hakan.

Tun da farko daraktan gidauniyar Bill and Melinda Gates a Nijeriya, Jeremie Zoungrana, ya nuna farin cikinsa bisa shaida sanya hannun da suka yi

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya
Rahotonni

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

October 4, 2025
Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin
Rahotonni

Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin

October 3, 2025
Next Post
An Kashe ‘Yan Boko Haram 49 A Sansaninsu 3 Yayin Luguden Wuta Ta Sama

An Kashe 'Yan Boko Haram 49 A Sansaninsu 3 Yayin Luguden Wuta Ta Sama

LABARAI MASU NASABA

…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version