Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Gidauniyar Ogan Boyen Kwankwasiyya Da “YOMPON” Sun Ba Marasa Lafiya 1,500 Magani Kyauta A Kaura Goje

by
1 year ago
in LABARAI
1 min read
Boye
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Daga Ibrahim Muhammad,

Gidauniyar Ogan Boyen Kwankwasiyya karkashin Alhaji Yusuf Imam da hadin-gwiwar Kungiyar matasa likitoci ta “YOMPON” sun gudanar da duba marasa lafiya kyauta da kuma basu magani.

Duba marasa lafiyan da suka kunshi maza da mata yara da manya an gudanar da shi ne a filin shinge dake mazabar Kaura Goje a karamar hukumar Nasatawa ranar Asabar.

Labarai Masu Nasaba

Tukunyar Gas Ce Ta Fashe Ba Bam Ba —Kwamishinan ‘Yan Sandan Kano

Wani Bam Ya Fashe A Sabon Garin Jihar Kano

Da yake bayani ga wakilimmu akan makasudin gudanar da tsarin na duba lafiya da bada magani kyauta, shugaban gidauniyar Ogan Boye, Hon Abdullahi  Kamal Ali ya ce, shirin na jinkai ne da Gidauniyar   ta saba gudanarwa a fannoni daban-daban.

Ya ce, dama kungiyar matasa likitoci sun saba yin irin wannan fita dan taimakawa marasa lafiya.Dan haka suka nemi hadin gwiwa da Gidauniyar Ogan Boye domin gudanar da duba matasa lafiya a Karamar hukumar Nasarawa.

Ya ce shugaban Gidauniyar na Ogan Boye Alhaji Yusuf Imam ya sahale ayi aikin duba marasa Lafiyan da mutum sama da 1,500 suka amfana da magani kyauta.

Ya ce, likitoci guda 50 ne suka yi aikin akan kowace irin cuta  da take damun mutum, wacce ake iya bada maganinta nan take aka bayar, wanda kuma take da bukatar zuzzurfan bincike za a tura Asibiti don kulawa da marasa lafiyan a karkashin gidauniyar.

Wadanda suka amfana da wannan tagomashi na duba lafiya da basu magani kyauta sun yaba tare da godewa Alhaji Yusuf Ogan Boye bisa wannan kulawa da ya yi musu tare da yi masa addu’ar Allah ya biya mass bukatunsa.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Daga Darajar Masarautar Rano A Gwamnatin APC Nasarar Ganduje Ce -Hon Idi Gwangwan

Next Post

Gwamnatin Gombe Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da NNPC Kan Samar Da Mai Daga Tsirrai

Labarai Masu Nasaba

Wani Bam Ya Fashe A Sabon Garin Jihar Kano

Tukunyar Gas Ce Ta Fashe Ba Bam Ba —Kwamishinan ‘Yan Sandan Kano

by
6 hours ago
0

...

Wani Bam Ya Fashe A Sabon Garin Jihar Kano

Wani Bam Ya Fashe A Sabon Garin Jihar Kano

by
8 hours ago
0

...

Yanzu-yanzu: EFCC Ta Cafke Akanta Janar Na Kasa, Ahmed Idris Bisa Zargin Badakala

Yanzu-yanzu: EFCC Ta Cafke Akanta Janar Na Kasa, Ahmed Idris Bisa Zargin Badakala

by Khalid Idris Doya
19 hours ago
0

...

Jami’an Tsaro Sun Kama Buduwar Da Ta Yi Batanci Ga Fiyayyen Halitta A Maiduguri

Jami’an Tsaro Sun Kama Buduwar Da Ta Yi Batanci Ga Fiyayyen Halitta A Maiduguri

by
1 day ago
0

...

Next Post
Tsirrai

Gwamnatin Gombe Za Ta Yi Hadin Gwiwa Da NNPC Kan Samar Da Mai Daga Tsirrai

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: