Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

Gidauniyar Sardauna Ta Ziyarci Gwamna Al-Makura

by Tayo Adelaja
September 27, 2017
in RAHOTANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Zubairu T. M. Lawal, Lafia

Gidauniyar Sir Ahmadu Bello Sardaunar Sakkwato karkashin Jagorancin Tsohon Mai shari’a Alhaji Mamman Nasir Galadiman Katsina, ta ziyarci gwamnan Jihar Nasarawa Alhaji Umar Tanko Al-makura a gidan gwamnati da ke garin Lafia.

samndaads

Da yake jawabi yayin ziyarar, shugaban tawagar Alhaji Mamman Nasir ya ce; “Makasudin zuwanmu shi ne hada danganataka mai karfi tsakanin wannan gidauniya da Gwamnatin Jihar Nasarawa”.

Tare da cewa; “Makasudin kafa wannan gidauniyar shi ne yadda yanzu wasu ke kokarin ganin an raba kasar nan  ba tare da sun san wahalar da magabata suka sha wajen hada kasar ta zama dunkulalliyar kasa daya ba”.

Shi ma da yake jawabi, Gwamnan Jihar Nasarawa Alhaji Umar Tanko Al-makura, ya jinjina wa wannan tawagar ta Gidauniyar Sardauna, saboda yadda ta dauki matakin hada kan al’ummar kasar nan ta yadda za a fahimci juna a zauna lafiya . A A cewar gwamnan, Sardaunan Sakkwato Sir Ahmadu Bello, ya yi aiki tukuru wajen ganin kan ‘yan kasa ya hade ba tare da nuna bambancin addini ko kabila ba.

Haka nan, ya ce  Gwamnatin Jihar Nasarawa za ta hada hannu da wannan gidauniyar wajen tunawa da ayyukan Sardaunan Sakkwato, domin cinma burin samar da zaman lafiya  da cigaban tattalin arzikin Arewa da kasa baki daya gami da samar da matsaya guda.

Gwamna Al-makura ya ce, tun lakocin da ya kama mulkin jiharsa ba shi da wani buri wuce samar da zaman lafiya da hadin kan al’ummar. Saboda a cewarsa, wannan shi ne koyi da ayyukan alheri na marigayi Sir Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato kuma shi ma tafarkin da kama kenan.

SendShareTweetShare
Previous Post

’Yan Kasuwar Kwari Sun Koka Kan Rashin Gudanar Da Zabe

Next Post

Al’ummar Dogon Dawa Sun Koka Kan Rashin Wutar Lantarki

RelatedPosts

Garban

Garban Kauye Farawa Ne Allurar Dinke Barakar Kumbotso – Muslihu Yusuf Ali

by Muhammad
10 hours ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, An bayyana zaben Sabon shugaban Karamar...

Harkokin Noma

Sarkin Noma Ya Shawarci Gwamnatin Tarayya Ta Kara Kokari Wajen Gyara Harkokin Noma

by Muhammad
11 hours ago
0

Daga Bala Kukkuru, Sarkin Noman Jihar Kano, Alhaji Yusuf Umar...

Kwazon Tambuwal

Hobbasar Kwazon Tambuwal Na Fara Biyan Albashi Daga Haraji A 2023

by Muhammad
1 day ago
0

Daga, Sharfaddeen Sidi Umar, Gwamnatin Jihar Sakkwato a karkashin jagorancin...

Next Post

Al’ummar Dogon Dawa Sun Koka Kan Rashin Wutar Lantarki

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version