Gina Al’ummar Sin Da Afrika Mai Makoma Ta Bai Daya, Zai Kai Afrika Ga Samun Tsaro Da Wadata Tamkar Kasar Sin
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gina Al’ummar Sin Da Afrika Mai Makoma Ta Bai Daya, Zai Kai Afrika Ga Samun Tsaro Da Wadata Tamkar Kasar Sin

byCMG Hausa
3 years ago
Kasar Sin

Shugaban kasar Sin ya jaddada muhimmancin hadin gwiwar tsaro da zaman lafiya tsakanin Sin da Afrika, tare da gabatar da shawarar gina al’ummar Sin da Afrika mai makoma ta bai daya a sabon zamani, domin cimma tsaro na bai daya. Shugaban ya bayyana haka ne yayin taro karo na biyu na ministocin kasashen Sin da Afrika kan dangantakar tsaro da zaman lafiya. 

Amini na kwarai shi ke kasancewa da amininsa a ko wanne hali. Matsalar tsaro batu ne da ke ciwa kasashen Afrika tuwo a kwarya, la’akari da mummunan tasirinta ga zaman lafiya da ci gaba. Babu wata kasa da za ta samu ci gaban da take muradi, muddun ta na fama da matsalar tsaro. Don haka a matsayinta na Aminiya ga kasashen Afrika, kuma babbar kasar da ta san ya kamata, Sin na kokarin hada gwiwa da su domin magance matsalar.

  • Kasar Sin Ta Harba Muhimmin Bangare Na Dakin Bincike Na Farko Na Tashar Sararin Samaniyarta

Kasar Sin ce kasa mafi yawan jama’a a duniya, amma kuma, tana cikin kasashe kalilan dake more zaman lafiya da tsaro a duniya. Yadda kasar Sin ta ke kokarin karfafa hadin gwiwar tsaro da zaman lafiya da kasashen Afrika, ya nuna cewa ta damu da yanayin da suke ciki, kuma tana muradin taimaka musu.

Har ila yau, kasashen Afrika da Sin na da kamanceceniya ta fuskar yawan al’umma, kuma kasashe masu tasowa, wannan ya samar wa kasashen Afrika wata dama mai sauki na koyi tare da aiwatar da dabarun Sin ba tare da samun matsala ba.

Taimakon kasar Sin daya ne daga cikin kyawawan manufofinta da suka saba da na kasashen yamma, wadanda suke ingiza rikici da yin katsalandan cikin harkokin gidan kasashe, har ma da rura wutar rikici da uwa uba kitsa juyin mulki.

Ko da yake, wanda ya gaza tabbatar da tsaro da zaman lafiya da kare al’ummarsa, ina zai samu gogewar bayar da shawara ko kuma zama abun koyi?
Duk wanda yake bibiyar kasar Sin, ko yake zaune a kasar, dole ne ya jinjinawa irin kwanciyar hankalin dake akwai.

Alkaluman kididdiga sun shaida cewa, yadda al’umma suke jin dadin yanayin tsaro a kasar Sin, ya karu zuwa kaso 98.62 a shekarar 2021, daga kaso 87.55 da ya kasance a shekarar 2012.

A ganina, hadin gwiwa a fannin tsaro da kasar Sin, abu ne da ya kamata gwamnatocin Afrika su dauka da muhimmanci idan suna son shawo kan matsalolin da ke addabarsu.

Shawarar gina al’ummar Sin da Afrika mai makoma ta bai daya da shugaba Xi Jinping ya gabatar, ba makawa kyakkyawar dabara ce da zata yi gagarumin tasiri a Afrika.

Wannan na nufin samun tsaro kamar kasar Sin har ma da ci gaba da kwanciyar hankali da wadata tamkar kasar Sin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa
Daga Birnin Sin

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Next Post
Gwamnatin Kaduna Ta Ba Da Hutun Kwana 3 Don Jama’a Su Yi Rijistar Katin Zabe

Gwamnatin Kaduna Ta Ba Da Hutun Kwana 3 Don Jama'a Su Yi Rijistar Katin Zabe

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version