Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Ginin Kasuwar Damaturu Ya Kankama

by
2 years ago
in RIGAR 'YANCI
2 min read
Ginin Kasuwar Damaturu Ya Kankama
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

A halin da ake ciki tunin aiki gina sabuwar kasuwar garin Damaturu Shalkwatar Jihar Yobe ya yi nisa amma har ya zuwa yanzu nafi yawa daga cikin masu shagunan da aka rushe don gina sabuwar kasuwar na kokawa bisa ga rashin biyansu kudadensu na shagunan su da aka rushe tare da zargin cewar gwamnatin Jihar ta yi ko oho bisa biyansu hakkokinsu duk cewar a cikin bayaninsa ga ‘yan kasuwar a cikin wani shiri Na tambaya da amsa da gidan Rediyo mallakar Jihar (YBC ) ya shirya yadda mai girma gwamna. Jihar Mai Mala Buni ya halatta, ya ambata cewar a sanin sa tuning an cire kudaden ma’aikatan don biyansa hakkokinsu.

Kan haka ne wakilinmu ya samu tattaunawa da shugaban kungiyar  ‘yan Kasuwar Damaturu Alhaji Kale Alhaji Bukar dangane da wannan lamari a matsayinsa na Wanda ke cikin mambobin kwamitin biyan ‘yan kasuwar hakkokinsu, yadda shugaban ya yi Karin haske kan wannan batu da cewar, a saninsa an gwamnatin Jihar Yobe lokacin tsohon gwamna Alhaji Ibrahim Gaidam ta ce ta ware kimanun Naira Miliyan 180 ne don biyan ‘yan kasuwar hakkokinsu.

Shugaban ya kara da cewar, cikin shaguna 658 da aka da su a kasuwar an biya ma su shaguna 248 zunzurutun kudi har Naira Miliyan 120 saura shaguna 409 da masu shi ba a biya su ba wadda kudin da ya rage a cewar kwamitin saura Naira Miliyan 66 wadda su din ma har ya zuwa yau din.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Jihar Zamfara Ta Tabbatar Da Kama  Wasu Sojoji Masu Hulda Da ‘Yan Ta’adda

Kansila Mai Mataimaka 18 Ya Sadaukar Da Albashinsa Na Farko

Alhaji Kale ya kara da cewar, kan wannan lamari shi da kansa ya jagoranci tawagar wasu ‘yan kasuwar ya zuwa zauren majalisar dokokin Jihar don mika kokensu ka kakakin majalisar yadda kakaki. Majalisar ya basu tabbacin yin wani abu akai, hakan kuwa aka yi domin kuwa majalisar ta kai ga saduwa ga gwamna Buni, ya kuma tabbatar da yin wani Abu akai.

Ya kara da cewar,  gwamna Mai Mala a hirarsa a cikin gidan Rediyon Jihar ya bayyana cewar,  a saninsa sun kammala biyan dukkannin hakkokinsu ‘yan kasuwar to amma kuma zai sake duba lamarin don yin wani abu a kai.

Don haka ne a cewarsa shi kansa ba a kai ga biyan sa  kudin shagonsa ba har ya zuwa yanzu ballantana ma a hada baki da shi don danne hakkokin ‘yàn uwansa ‘yan kasuwar kamar yadda wasu ke zargin sa a kai saboda rashin sani.

Shugaban ya yi da babbar muryaa gs gwamnan Jihar Alhaji Mai Mala Buni kan ya kawo musu dauki ta wajen gano su waye hakkokin ’yan kasuwar kW hannunsu domin a cewaraa da yawa cikin ‘yan kasuwar sanadiyyar hakan sun rasa rayukansu yayin da wassu kuma suka rasa lafiyarsu.

Kale ya kara da cewar, duba da yadda lamurra suka tabarbare kan hakan da yawan ‘yan kasuwar sun karye wato jarukansu sun Kate ta yadda babu a kanti babu a kanta.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Manoman Auduga 500 Za Su Samu Tallafin Bankin Najeriya A Neja

Next Post

Fatima Binta Bello Ta Burge Al’ummar Gombe Ta Kudu Da Takin Zamani

Labarai Masu Nasaba

Zamfara

Gwamnatin Jihar Zamfara Ta Tabbatar Da Kama  Wasu Sojoji Masu Hulda Da ‘Yan Ta’adda

by
1 year ago
0

...

Kansila Mai Mataimaka 18 Ya Sadaukar Da Albashinsa Na Farko

by
1 year ago
0

...

APC

Sanata Al-Makura Ya Cancanci Rike Kujerar Shugabancin APC, Inji Gwamna Sule

by
1 year ago
0

...

Kebbi

Bagudu Ya Bukaci ’Yan Nijeriya Su Zama Masu Kishin Kasa A Shafukan Sada Zumunta

by
1 year ago
0

...

Next Post
Haramta Shigo Da Taki Na Iya Gurgunta Noma A Nijeriya – Masana

Fatima Binta Bello Ta Burge Al’ummar Gombe Ta Kudu Da Takin Zamani

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: