Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Girma Ya Fadi

by
1 year ago
in DAGA BIRNIN SIN
2 min read
Ana Bacin Rai Game Da Yadda Amurka Ke Mallake Rigakafin Fiye Da Kima Yayin Da Annoba Ke Kara Kamari A Duniya
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Labarai Masu Nasaba

Yau Ake Cika Shekaru Hudu Da Kafa Kwamitin Kula Da Harkokin Waje Na Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin

Kasashen BRICS Sun Yi Kira A Hada Kai Don Tinkarar Sauyin Yanayi

Daga Ibrahim Yaya

A yayin da kasashen duniya irinsu kasar Sin ke rabawa tare da sayar da alluran riga kafin annobar COVID-19 da suka samar ga kasashe mabukata da kawayensu, ita kuma Amurka dake zama babbar kasa a duniya, tana boye riga kafin ne, maimakon ta taimakawa kasashe masu bukata ko ma ta yiwa al’ummominta alluran riga kafin.
Wannan mataki da mahukuntan kasar Amurka suka dauka, ya sa jama’a bayyana fushi da suka ta kafofin sada zumunta, kan yadda Amurkar da ma kasashen yammacin duniya suke boye alluran riga kafin COVID-19, matakin da kowa ke cewa gurguwar shawara ce, wadda ba za ta kai kasar ga gaci ba.
Hukumar lafiya ta duniya (WHO), ta sha yin kira ga manyan kasashe da ma kamfanonin dake samar da alluran riga kafin annobar, da su raba su bisa adalci da sauran kasashe, musamman kasashe masu tasowa. Wannan ne ma ya sa MDD take jagorantar shirin nan na COVAX, mai raba riga kafin ga kasashe bisa daidaito da adalci, musamman kasashe masu tasowa.
Masu fashin bakin dai, sun yaba kokarin kasar Sin, bisa cika alkawatin da ta yi tun farko cewa, da zarar ta gudanar da bincike ta kuma samar da riga kafin, to zai kasance hajar al’ummar duniya.
Wannan gurguwar shawara da Amurka ta dauka na boye riga kafin, ba zai kasance mai fa’ida ga hadin gwiwar kasa da kasa kan yaki da wannan annoba ba. Yanzu haka, annobar ta sake bulla a karo na uku a kasar Indiya, inda take ci gaba da hallaka rayukan jama’a, baya ga sauran kasashe dake fama da wannan annoba.
Wani rahoto da jaridar Times of India (TOI) ta wallafa, ya bayyana cewa, ana ta kara wallafa rahotannin kin jikin Amurka da na kasashen yamma a kafofin sada zumunta, tare da sukar gwamnatin Biden da Harris, kan yadda suka boye tarin alluran riga kafin ba tare da an fitar da su don a yiwa jama’a ba.
Haka kuma, Amurka ta toshe kunnenta kan yadda cutar ke kara tsananta a kasashe kamar Indiya da Brazil, wadanda ke zama na daya da na biyu bi da bi da cutar ta fi kamari a duniya.
Cibiyar nan ta Duke ta kasa da kasa mai kula da harkar kiwon lafiya, ta ce jaridar TOI ta yi nuni da cewa, Amurka za ta kara samun alluran riga kafin fiye da kima har sama da miliyan 300 ko wasu karin riga kafin nan da watan Yuli, yayin da kasashe da dama sai sun jira shekaru, kafin su kammala yin riga kafin a kasashensu. Bari kashi a ciki dai ba ya maganin Yunwa. (Ibrahim Yaya)

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Batun Takarar Manyan Kasashen Duniya A Nahiyar Afirka Da Amurka Ta Tabo Zai Haifar Da Illa Ga Moriyar Kasashen Afirka

Next Post

Darektar WTO: Neman Dakushe Sin A Fannin Gyare-Gyaren Ciniyayya Ba Zai Yi Nasara Ba

Labarai Masu Nasaba

Yau Ake Cika Shekaru Hudu Da Kafa Kwamitin Kula Da Harkokin Waje Na Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin

Yau Ake Cika Shekaru Hudu Da Kafa Kwamitin Kula Da Harkokin Waje Na Jam’iyyar Kwaminis Ta Kasar Sin

by CMG Hausa
15 hours ago
0

...

Kasashen BRICS Sun Yi Kira A Hada Kai Don Tinkarar Sauyin Yanayi

Kasashen BRICS Sun Yi Kira A Hada Kai Don Tinkarar Sauyin Yanayi

by CMG Hausa
16 hours ago
0

...

Al’ummar Afirka Ba Su Bukatar A Yi Musu Lacca

Al’ummar Afirka Ba Su Bukatar A Yi Musu Lacca

by CMG Hausa
18 hours ago
0

...

Masana sun yi Allah wadai da yunkurin Amurka na neman dakile cigaban al’ummar Xinjiang

Masana sun yi Allah wadai da yunkurin Amurka na neman dakile cigaban al’ummar Xinjiang

by CMG Hausa
18 hours ago
0

...

Next Post
Darektar WTO: Neman Dakushe Sin A Fannin Gyare-Gyaren Ciniyayya Ba Zai Yi Nasara Ba

Darektar WTO: Neman Dakushe Sin A Fannin Gyare-Gyaren Ciniyayya Ba Zai Yi Nasara Ba

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: